< 2 Chroniques 29 >

1 Ézéchias commença de régner étant âgé de 25 ans; et il régna 29 ans à Jérusalem; et le nom de sa mère était Abija, fille de Zacharie.
Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
2 Et il fit ce qui est droit aux yeux de l’Éternel, selon tout ce qu’avait fait David, son père.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
3 La première année de son règne, au premier mois, il ouvrit les portes de la maison de l’Éternel, et les répara.
A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
4 Et il fit venir les sacrificateurs et les lévites, et les assembla sur la place orientale,
Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
5 et leur dit: Écoutez-moi, Lévites! Maintenant, sanctifiez-vous, et sanctifiez la maison de l’Éternel, le Dieu de vos pères, et jetez la souillure hors du sanctuaire.
ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
6 Car nos pères ont été infidèles, et ont fait ce qui est mauvais aux yeux de l’Éternel, notre Dieu, et l’ont abandonné, et ont détourné leurs faces de la demeure de l’Éternel, et lui ont tourné le dos.
Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
7 Même ils ont fermé les portes du portique, et ont éteint les lampes, et n’ont pas fait fumer l’encens, et n’ont pas offert l’holocauste dans le lieu saint au Dieu d’Israël.
Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
8 Et la colère de l’Éternel a été sur Juda et sur Jérusalem, et il les a livrés à la vexation et à la destruction et au sifflement, comme vous le voyez de vos yeux.
Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
9 Et voici, à cause de cela, nos pères sont tombés par l’épée, et nos fils, et nos filles, et nos femmes, sont en captivité.
Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
10 Maintenant, j’ai à cœur de faire alliance avec l’Éternel, le Dieu d’Israël, afin que l’ardeur de sa colère se détourne de nous.
Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
11 Maintenant, mes fils, ne soyez pas négligents, car c’est vous que l’Éternel a choisis, pour que vous vous teniez devant lui pour le servir, et pour être ses serviteurs et ceux qui lui offrent [ce qui se brûle sur l’autel].
’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
12 Et les lévites se levèrent, Makhath, fils d’Amasçaï, et Joël, fils d’Azaria, d’entre les fils des Kehathites; et d’entre les fils de Merari, Kis, fils d’Abdi, et Azaria, fils de Jehalléleël; et d’entre les Guershonites, Joakh, fils de Zimma, et Éden, fils de Joakh;
Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
13 et d’entre les fils d’Élitsaphan, Shimri et Jehiel; et d’entre les fils d’Asaph, Zacharie et Matthania;
Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
14 et d’entre les fils d’Héman, Jekhiel et Shimhi; et d’entre les fils de Jeduthun, Shemahia et Uziel.
Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
15 Et ils rassemblèrent leurs frères, et se sanctifièrent; et ils entrèrent selon le commandement du roi, d’après les paroles de l’Éternel, pour purifier la maison de l’Éternel.
Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
16 Et les sacrificateurs entrèrent dans l’intérieur de la maison de l’Éternel, pour la purifier, et jetèrent dehors, au parvis de la maison de l’Éternel, toutes les impuretés qu’ils trouvèrent dans le temple de l’Éternel, et les lévites les prirent pour les jeter dehors dans le torrent du Cédron.
Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
17 Et ils commencèrent la sanctification le premier [jour] du premier mois, et au huitième jour du mois ils vinrent au portique de l’Éternel, et sanctifièrent la maison de l’Éternel pendant huit jours; et, le seizième jour du premier mois, ils eurent achevé.
Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
18 Et ils entrèrent chez le roi Ézéchias, et dirent: Nous avons purifié toute la maison de l’Éternel, et l’autel de l’holocauste et tous ses ustensiles, et la table des [pains] à placer en rangées et tous ses ustensiles;
Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
19 et nous avons mis en état et sanctifié tous les ustensiles que le roi Achaz avait rejetés pendant son règne, pendant son péché; et voici, ils sont devant l’autel de l’Éternel.
Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
20 Et le roi Ézéchias se leva de bonne heure, et assembla les chefs de la ville, et monta à la maison de l’Éternel.
Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
21 Et ils amenèrent sept taureaux, et sept béliers, et sept agneaux, et sept boucs en sacrifice pour le péché, pour le royaume, et pour le sanctuaire, et pour Juda. Et [le roi] dit aux sacrificateurs, fils d’Aaron, de les offrir sur l’autel de l’Éternel.
Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
22 Et ils égorgèrent les bœufs, et les sacrificateurs reçurent le sang, et en firent aspersion sur l’autel; et ils égorgèrent les béliers et firent aspersion du sang sur l’autel; et ils égorgèrent les agneaux et firent aspersion du sang sur l’autel;
Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
23 et ils firent approcher les boucs du sacrifice pour le péché, devant le roi et la congrégation, et ils posèrent leurs mains sur eux;
Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
24 et les sacrificateurs les égorgèrent et firent avec leur sang, sur l’autel, la purification du péché, afin de faire propitiation pour tout Israël; car le roi avait dit que l’holocauste et le sacrifice pour le péché seraient pour tout Israël.
Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
25 Et il plaça les lévites dans la maison de l’Éternel, avec des cymbales, des luths et des harpes, selon le commandement de David, et de Gad, le voyant du roi, et de Nathan, le prophète; car le commandement était de la part de l’Éternel par ses prophètes.
Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
26 Et les lévites se tinrent là avec les instruments de David, et les sacrificateurs avec les trompettes.
Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
27 Et Ézéchias dit d’offrir l’holocauste sur l’autel; et, au moment où commença l’holocauste, le cantique de l’Éternel commença, et les trompettes avec l’accompagnement des instruments de David, roi d’Israël.
Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
28 Et toute la congrégation se prosterna, et le cantique se chanta, et les trompettes sonnèrent, tout le temps, jusqu’à ce que l’holocauste soit achevé.
Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
29 Et quand on eut achevé d’offrir l’holocauste, le roi et tous ceux qui se trouvaient avec lui s’inclinèrent et se prosternèrent.
Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
30 Et le roi Ézéchias et les chefs dirent aux lévites de louer l’Éternel avec les paroles de David et d’Asaph, le voyant; et ils louèrent avec joie, et ils s’inclinèrent et se prosternèrent.
Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
31 Et Ézéchias prit la parole et dit: Vous vous êtes maintenant consacrés à l’Éternel; approchez-vous, et amenez des sacrifices et des offrandes de louanges dans la maison de l’Éternel. Et la congrégation amena des sacrifices et des offrandes de louanges, et tous ceux qui avaient un esprit libéral [amenèrent] des holocaustes.
Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
32 Et le nombre des holocaustes que la congrégation amena fut de 70 taureaux, 100 béliers, 200 agneaux, tout cela pour l’holocauste à l’Éternel.
Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
33 Et les choses consacrées furent 600 bœufs et 3 000 moutons.
Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
34 Seulement il y avait trop peu de sacrificateurs, et ils ne purent écorcher tous les holocaustes; et leurs frères, les lévites, les aidèrent, jusqu’à ce que l’ouvrage soit achevé et que les sacrificateurs se soient sanctifiés; car les lévites furent plus droits de cœur que les sacrificateurs pour se sanctifier.
Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
35 Et il y eut aussi des holocaustes en abondance, avec les graisses des sacrifices de prospérités, et avec les libations pour les holocaustes. Et le service de la maison de l’Éternel fut rétabli.
Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
36 Et Ézéchias et tout le peuple se réjouirent de ce que Dieu avait disposé le peuple; car la chose fut faite soudainement.
Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.

< 2 Chroniques 29 >