< 2 Chroniques 24 >

1 Joas était âgé de sept ans lorsqu’il commença de régner; et il régna 40 ans à Jérusalem; et le nom de sa mère était Tsibia, de Beër-Shéba.
Yowash yana da shekara goma sha bakwai sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarauta a Urushalima shekara arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; ita daga Beyersheba.
2 Et Joas fit ce qui est droit aux yeux de l’Éternel, tous les jours de Jehoïada, le sacrificateur.
Yowash ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji duka shekarun Yehohiyada firist.
3 Et Jehoïada prit deux femmes pour [Joas], et il engendra des fils et des filles.
Yehohiyada ya zaɓi mata biyu dominsa, yana kuma da’ya’ya maza da’ya’ya mata.
4 Et il arriva, après cela, que Joas eut à cœur de restaurer la maison de l’Éternel.
Wani lokaci daga baya Yowash ya yanke shawara yă gyara haikalin Ubangiji.
5 Et il assembla les sacrificateurs et les lévites, et leur dit: Allez par les villes de Juda, et recueillez de l’argent de tout Israël, pour réparer la maison de votre Dieu, d’année en année, et hâtez cette affaire. Mais les lévites ne la hâtèrent point.
Ya tara firistoci da Lawiyawa wuri ɗaya ya ce musu, “Ku je garuruwan Yahuda ku karɓa kuɗin da ya kamata a biya shekara-shekara daga dukan Isra’ila, don gyaran haikalin Allahnku. Ku yi haka yanzu.” Amma Lawiyawa ba su yi haka nan da nan ba.
6 Et le roi appela Jehoïada, le chef, et lui dit: Pourquoi n’as-tu pas exigé des lévites qu’ils apportent, de Juda et de Jérusalem, le tribut de Moïse, serviteur de l’Éternel, [imposé à] la congrégation d’Israël pour la tente du témoignage?
Saboda haka sarki ya kira Yehohiyada babban firist ya ce masa, “Me ya sa ba ka bukaci Lawiyawa su kawo harajin da Musa bawan Ubangiji ya ce a biya daga Yahuda da Urushalima da kuma taron Isra’ila domin Tentin Sujada Shaida ba?”
7 Car Athalie, cette méchante femme, [et] ses fils, avaient dévasté la maison de Dieu, et, toutes les choses saintes de la maison de l’Éternel, ils les avaient aussi employées pour les Baals.
Yanzu’ya’ya muguwar macen nan Ataliya maza sun fasa zuwa cikin haikalin Allah, suka kuma yi amfani da kayayyaki masu tsarki ma wa Ba’al.
8 Et le roi commanda, et on fit un coffre, et on le mit à la porte de la maison de l’Éternel, en dehors.
Bisa ga umarnin sarki, aka yi akwati aka sa a waje, a mashigin haikalin Ubangiji.
9 Et on publia dans Juda et dans Jérusalem qu’on apporte à l’Éternel le tribut de Moïse, serviteur de Dieu, [imposé] à Israël, dans le désert.
Aka yi umarni a Yahuda da Urushalima cewa ya kamata suka kawo wa Ubangiji harajin da Musa bawan Allah ya bukaci daga Isra’ila a hamada.
10 Et tous les princes et tout le peuple s’en réjouirent; et ils apportèrent [l’argent] et le jetèrent dans le coffre, jusqu’à ce qu’on ait fini.
Dukan hafsoshi da dukan mutane suka kawo nasu kuɗin da aka sa musu da farin ciki, suna zuba su cikin akwatin sai da ya cika.
11 Et il arrivait que, lorsque c’était le temps d’apporter le coffre au contrôle du roi, par la main des lévites, et qu’on voyait qu’il y avait beaucoup d’argent, le secrétaire du roi et l’officier du principal sacrificateur venaient et vidaient le coffre; et ils le reportaient et le remettaient à sa place. Ils faisaient ainsi jour par jour, et on recueillit de l’argent en abondance.
Duk sa’ad da Lawiyawa suka fito da akwatin zuwa ga hafsoshin sarki, suka kuma ga cewa akwatin yana da kuɗi mai yawa, sai magatakardan fada da hafsan babban firist su zo su juya kuɗin daga akwatin su mai da shi wurinsa. Sun riƙa yin haka kullum suka tara kuɗi mai yawa.
12 Et le roi et Jehoïada le donnaient à ceux qui faisaient l’ouvrage du service de la maison de l’Éternel, et ceux-ci prenaient à gage des tailleurs de pierres et des charpentiers pour restaurer la maison de l’Éternel, et aussi des ouvriers en fer et en airain pour réparer la maison de l’Éternel.
Sarki da Yehohiyada suka ba da shi ga mutanen da suka yi aikin da ake bukata don haikalin Ubangiji. Suka ɗauki masu gini da kafintoci don su gyara haikalin Ubangiji, da kuma ma’aikatan ƙarafa da tagulla don su gyara haikalin.
13 Et ceux qui faisaient l’ouvrage travaillèrent, et l’œuvre de restauration se fit par leur moyen, et ils rétablirent la maison de Dieu en son état, et la consolidèrent.
Mutanen da suke lura da aikin natsattsu ne, kuma gyare-gyaren suka ci gaba a ƙarƙashinsu. Suka sāke gina haikalin Allah bisa ga ainihin fasalinsa suka ƙara masa ƙarfi.
14 Et quand ils eurent achevé, ils apportèrent devant le roi et devant Jehoïada le reste de l’argent; et on en fit des ustensiles pour la maison de l’Éternel, des ustensiles pour le service et pour les holocaustes, et des coupes, et des ustensiles d’or et d’argent. Et on offrit des holocaustes dans la maison de l’Éternel continuellement, tous les jours de Jehoïada.
Da suka gama, suka kawo sauran kuɗin wa sarki da Yehohiyada, da su ne kuwa aka yi kayayyaki domin hidima da kuma domin hadayun ƙonawa, haka kuma kwanoni da sauran kayayyakin zinariya da azurfa. Muddin Yehohiyada yana raye, aka riƙa kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
15 Et Jehoïada devint vieux et rassasié de jours, et il mourut. Il était âgé de 130 ans quand il mourut.
Yanzu Yehohiyada ya tsufa kuma cike da shekaru, ya kuwa mutu yana da shekara ɗari da talatin.
16 Et on l’enterra dans la ville de David avec les rois, car il avait fait du bien en Israël, et pour Dieu et pour sa maison.
Aka binne shi tare da sarakuna a cikin Birnin Dawuda, saboda kirkin da ya yi a Isra’ila wa Allah da haikalinsa.
17 Et après la mort de Jehoïada, les chefs de Juda vinrent et s’inclinèrent devant le roi; alors le roi les écouta.
Bayan mutuwar Yehohiyada, hafsoshin Yahuda suka zo suka yi mubaya’a wa sarki, ya kuma saurare su.
18 Et ils abandonnèrent la maison de l’Éternel, le Dieu de leurs pères, et servirent les ashères et les idoles; et il y eut de la colère contre Juda et contre Jérusalem, parce qu’ils s’étaient rendus coupables en cela.
Suka yashe haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa ginshiƙan Ashera da kuma gumaka. Saboda laifinsu, fushin Allah ya sauko a kan Yahuda da Urushalima.
19 Et l’Éternel envoya parmi eux, pour les ramener à lui, des prophètes qui témoignèrent contre eux; mais ils n’écoutèrent point.
Ko da yake Ubangiji ya aiki annabawa zuwa wurin mutane don su dawo da su gare shi, kuma ko da yake sun ba da shaida a kansu, ba su saurara ba.
20 Et l’Esprit de Dieu revêtit Zacharie, fils de Jehoïada, le sacrificateur, et il se tint debout au-dessus du peuple, et leur dit: Ainsi dit Dieu: Pourquoi transgressez-vous les commandements de l’Éternel? Vous ne réussirez point; car vous avez abandonné l’Éternel, et il vous abandonnera aussi.
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’”
21 Et ils conspirèrent contre lui, et le lapidèrent avec des pierres par l’ordre du roi, dans le parvis de la maison de l’Éternel.
Amma suka yi masa maƙarƙashiya, kuma ta wurin umarnin sarki suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu a filin haikalin Ubangiji.
22 Et le roi Joas ne se souvint pas de la bonté dont Jehoïada, père de Zacharie, avait usé envers lui, et il tua son fils. Et comme il mourait, il dit: Que l’Éternel regarde et redemande!
Sarki Yowash bai tuna da alherin da Yehohiyada mahaifin Zakariya ya nuna masa ba, sai ya kashe ɗansa, wanda ya ce yayinda yake mutuwa, “Bari Ubangiji yă dubi wannan yă kuma sāka maka.”
23 Et il arriva, quand l’année fut révolue, que l’armée de Syrie monta contre Joas, et entra en Juda et à Jérusalem; et ils détruisirent d’entre le peuple tous les chefs du peuple, et envoyèrent toutes leurs dépouilles au roi, à Damas.
Da shekara ta kewaye, mayaƙan Aram suka yi gāba da Yowash suka kai hari wa Yahuda da Urushalima suka kuma kashe dukan shugabannin mutane, suka aika da dukan ganima zuwa ga sarkinsu a Damaskus.
24 Car l’armée de Syrie vint avec un petit nombre d’hommes, et l’Éternel livra en leurs mains une très grande armée, parce qu’ils avaient abandonné l’Éternel, le Dieu de leurs pères. Ainsi [les Syriens] firent justice de Joas.
Ko da yake mayaƙan Arameyawa sun zo da mutane kaɗan kawai, Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan sojojin Yahuda mafi yawa, don mutanen Yahuda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu, aka kuma hukunta Yowash.
25 Et quand ils l’eurent quitté, (or ils l’avaient laissé dans de grandes maladies, ) ses serviteurs conspirèrent contre lui, à cause du sang des fils de Jehoïada, le sacrificateur; et ils le tuèrent sur son lit, et il mourut; et on l’enterra dans la ville de David, mais on ne l’enterra pas dans les sépulcres des rois.
Sa’ad da Arameyawa suka janye, suka bar Yowash da mummunan rauni. Hafsoshinsa suka haɗa baki a kansa saboda kisan ɗan Yehohiyada firist da ya yi, suka kashe shi a kan gadonsa. Ta haka ya mutu aka kuma binne shi makabartan sarakuna.
26 Et ce sont ici ceux qui conspirèrent contre lui: Zabad, fils de Shimhath, l’Ammonite, et Jozabad, fils de Shimrith, la Moabite.
Waɗanda suka haɗa bakin kuwa su ne Zabad ɗan Shimeyat wata mutuniyar Ammon da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab.
27 Et quant à ses fils, et à la grandeur du tribut qui lui fut imposé, et aux constructions de la maison de Dieu, voici, ces choses sont écrites dans les commentaires du livre des rois. Et Amatsia, son fils, régna à sa place.
Labarin’ya’yansa maza, annabce-annabce masu yawa game da shi, da tarihin gyaran haikalin Allah suna a rubuce a rubuce-rubuce a littafin sarakuna. Amaziya ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chroniques 24 >