< 2 Chroniques 2 >

1 Et Salomon résolut de bâtir une maison pour le nom de l’Éternel, et une maison pour son royaume.
Solomon ya ba da umarni don a gina haikali domin sunan Ubangiji da kuma fada wa kansa.
2 Et Salomon dénombra 70 000 portefaix, et 80 000 hommes qui taillaient [la pierre] sur la montagne, et 3 600 surveillants [préposés] sur eux.
Ya ɗebi mutane dubu saba’in su zama’yan ɗauko, mutane dubu tamanin su zama masu fasa dutse a tuddai, da kuma mutane dubu uku da ɗari shida su zama masu lura da su.
3 Et Salomon envoya vers Hiram, roi de Tyr, disant: [Fais pour moi] comme tu as fait pour David, mon père, à qui tu as envoyé des cèdres pour se bâtir une maison afin d’y habiter.
Solomon ya aika wannan saƙo ga Hiram sarkin Taya. “Ka aika mini gumaguman al’ul kamar yadda ka yi wa mahaifina Dawuda sa’ad da ka aika masa al’ul don yă gina fada yă zauna a ciki.
4 Voici, je bâtis une maison pour le nom de l’Éternel, mon Dieu, pour la lui consacrer, pour faire fumer devant lui l’encens de drogues odoriférantes, et pour l’arrangement continuel [des pains], et pour les holocaustes du matin et du soir, des sabbats, et des nouvelles lunes, et des jours solennels de l’Éternel, notre Dieu; cela est [prescrit] à Israël à toujours.
Yanzu ina shirin ginin haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe shi gare shi don ƙona turare mai ƙanshi a gabansa, don kuma ajiyar burodi mai tsarki kullum, da kuma don miƙa hadayun ƙonawa kowace safiya, kowace yamma, da a Asabbatai da Sababbin Wata, da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji Allahnmu. Wannan dawwammamiyar farilla ce don Isra’ila.
5 Et la maison que je bâtis sera grande; car notre Dieu est grand au-dessus de tous les dieux.
“Haikalin da zan gina zai zama mai girma, domin Allahnmu ya fi dukan sauran alloli girma.
6 Et qui a le pouvoir de lui bâtir une maison, car les cieux, et les cieux des cieux, ne peuvent le contenir? Et qui suis-je, moi, pour lui bâtir une maison, si ce n’est pour faire fumer [ce qui se brûle] devant lui?
Amma wa zai iya gina haikali dominsa, shi wanda sammai, har ma da sama sammai, ba za su iya riƙe shi ba? To, wane ne ni da zan gina haikali dominsa, in ba dai wurin ƙona hadayu a gabansa ba?
7 Et maintenant, envoie-moi un homme habile à travailler en or, et en argent, et en airain, et en fer, et en pourpre, et en cramoisi, et en bleu, et qui sache graver, avec les hommes habiles qui sont auprès de moi en Juda et à Jérusalem [et] que David, mon père, a préparés.
“Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanince a aiki da azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanince da aikin sassaƙa, domin yă yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuda da Urushalima, waɗanda mahaifina Dawuda ya tanada.
8 Et envoie-moi du Liban des bois de cèdres, de cyprès, et d’algummim; car je sais que tes serviteurs s’entendent à couper le bois dans le Liban; et voici, mes serviteurs seront avec tes serviteurs,
“Ka kuma aika mini al’ul, fir da gumaguman algum daga Lebanon, gama na san cewa mutanenka sun gwanince a yakan katakai a can. Mutanena kuwa za su yi aiki tare da naka
9 pour me préparer du bois en abondance; car la maison que je bâtis sera grande et merveilleuse.
don su tanada mini katakai da yawa, domin haikalin da zan gina dole yă zama mai girma da kuma ƙasaitacce.
10 Et voici, je donnerai à tes serviteurs, les coupeurs, qui abattront les bois, 20 000 cors de froment battu, et 20 000 cors d’orge, et 20 000 baths de vin, et 20 000 baths d’huile.
Zan ba wa bayinka masu yankan katakai waɗanda suka yanka katako, garwa niƙaƙƙen alkama dubu ashirin, garwan sha’ir dubu ashirin da randunan ruwan inabi dubu ashirin da kuma randunan man zaitun dubu ashirin.”
11 Et Hiram, roi de Tyr, dit dans un écrit qu’il envoya à Salomon: À cause de l’amour de l’Éternel pour son peuple, il t’a établi roi sur eux.
Hiram sarkin Taya ya amsa ta wurin rubuta wasiƙa zuwa ga Solomon. “Domin Ubangiji yana ƙaunar mutanensa, ya naɗa ka sarkinsu.”
12 Et Hiram dit: Béni soit l’Éternel, le Dieu d’Israël, qui a fait les cieux et la terre, de ce qu’il a donné au roi David un fils sage, doué de sens et d’intelligence, qui bâtira une maison à l’Éternel et une maison pour son royaume.
Hiram ya ƙara da cewa, “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya yi sama da ƙasa! Ya ba Sarki Dawuda ɗa mai hikima, cike da wayo da kuma sani, wanda zai gina haikali domin Ubangiji da kuma fada wa kansa.
13 Et maintenant je t’envoie un homme habile, doué d’intelligence, Huram-Abi,
“Zan aika maka Huram-Abi, wani gwani wanda ya iya aiki, kuma mai hikima,
14 fils d’une femme d’entre les filles de Dan, et dont le père est Tyrien, sachant travailler en or, et en argent, en airain, en fer, en pierres, et en bois, en pourpre, en bleu, et en byssus, et en cramoisi, et [sachant] faire toute sorte de gravure et inventer toute sorte de choses qu’on lui donnera à inventer, avec tes hommes habiles et les hommes habiles de mon seigneur David, ton père.
wanda mahaifiyarsa ta fito daga Dan, mahaifinsa kuma daga Taya. An horar da shi a aikin zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, dutse, itace, da kuma shuɗi, shunayya, garura, da lilin mai kyau. Ya gogu a kowane irin zāne-zāne, zai kuma iya yin kowane zānen da aka ba shi. Zai yi aiki tare da masu sana’arka, da kuma tare da waɗanda ranka yă daɗe, Dawuda mahaifinka ya tanada.
15 Et maintenant, que mon seigneur envoie à ses serviteurs le froment et l’orge, l’huile et le vin qu’il a dit;
“Yanzu fa, bari ranka yă daɗe, yă aiko wa bayinsa alkama da sha’ir da kuma man zaitun da ruwan inabin da ka alkawarta,
16 et nous, nous couperons des bois dans le Liban, autant que tu en auras besoin, et nous te les amènerons en radeaux sur la mer à Japho; et toi, tu les feras monter à Jérusalem.
za mu kuwa yanka dukan gumagumai daga Lebanon da kake bukata za mu kuwa yi fitonsu ta teku, su gangara zuwa Yaffa. Za ka iya kwashe su daga can ka haura zuwa Urushalima.”
17 Et Salomon dénombra tous les hommes étrangers qui étaient dans le pays d’Israël, suivant le dénombrement qu’en avait fait David, son père, et on en trouva 153 600.
Solomon ya ƙidaya dukan baƙin da suke cikin Isra’ila, bayan ƙidayan da mahaifinsa Dawuda ya yi; aka kuma tarar sun kai 153,600.
18 Et il en fit 70 000 portefaix, et 80 000 tailleurs de pierres sur la montagne, et 3 600 surveillants pour faire travailler le peuple.
Ya sa 70,000 a cikinsu su zama’yan ɗauko, 80,000 kuma su zama masu fasan dutse a tuddai, sa’an nan 3,600 su zama shugabanni masu lura da aiki.

< 2 Chroniques 2 >