< 2 Chroniques 13 >

1 La dix-huitième année du roi Jéroboam, Abija commença de régner sur Juda.
A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
2 Il régna trois ans à Jérusalem; et le nom de sa mère était Micaïa, fille d’Uriel, de Guibha. Et il y eut guerre entre Abija et Jéroboam.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
3 Et Abija commença la guerre avec une armée d’hommes de guerre, de 400 000 hommes d’élite; et Jéroboam se rangea en bataille contre lui avec 800 000 hommes d’élite, forts et vaillants.
Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
4 Et Abija se tint sur le haut de la montagne de Tsemaraïm, qui est dans la montagne d’Éphraïm, et dit: Écoutez-moi, Jéroboam et tout Israël!
Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
5 N’est-ce pas à vous de savoir que l’Éternel, le Dieu d’Israël, a donné à David la royauté sur Israël pour toujours, à lui et à ses fils, par une alliance de sel?
Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
6 Et Jéroboam, fils de Nebath, serviteur de Salomon, fils de David, s’est levé, et s’est révolté contre son seigneur;
Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
7 et des hommes de rien, des fils de Bélial, se sont assemblés vers lui; et ils se sont fortifiés contre Roboam, fils de Salomon; et Roboam était jeune et craintif; et il ne s’est pas montré fort devant eux.
sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
8 Et maintenant vous pensez vous montrer forts contre le royaume de l’Éternel, qui est dans la main des fils de David, et vous êtes une grande multitude, et vous avez avec vous les veaux d’or que Jéroboam vous a faits pour [être vos] dieux.
“Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
9 N’avez-vous pas chassé les sacrificateurs de l’Éternel, les fils d’Aaron, et les lévites? Et vous vous êtes fait des sacrificateurs, comme les peuples des [autres] pays; quiconque est venu avec un jeune taureau et sept béliers, pour être consacré, est devenu sacrificateur de ce qui n’est pas Dieu.
Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
10 Mais pour nous, l’Éternel est notre Dieu, et nous ne l’avons pas abandonné; et des sacrificateurs, fils d’Aaron, servent l’Éternel, et les lévites sont à leurs fonctions;
“Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
11 et chaque matin et chaque soir, ils font fumer les holocaustes à l’Éternel, et l’encens de drogues odoriférantes; et [nous avons] les pains rangés sur la table pure, et le chandelier d’or et ses lampes pour brûler chaque soir, car nous, nous faisons l’acquit de la charge que l’Éternel, notre Dieu, nous a confiée; mais vous, vous l’avez abandonné.
Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
12 Et voici, nous avons avec nous, à notre tête, Dieu et ses sacrificateurs, et les trompettes au son éclatant, pour sonner avec éclat contre vous. Fils d’Israël, ne faites pas la guerre contre l’Éternel, le Dieu de vos pères; car vous ne réussirez pas!
Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
13 Mais Jéroboam fit prendre un détour à une embuscade pour venir derrière eux; et ils étaient devant Juda, et l’embuscade était derrière eux.
To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
14 Et Juda se tourna, et voici, la bataille était contre eux, devant et derrière; et ils crièrent à l’Éternel, et les sacrificateurs sonnèrent des trompettes;
Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
15 et les hommes de Juda jetèrent des cris; et il arriva, comme les hommes de Juda jetaient des cris, que Dieu frappa Jéroboam et tout Israël, devant Abija et Juda.
mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
16 Et les fils d’Israël s’enfuirent devant Juda, et Dieu les livra en leurs mains.
Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
17 Et Abija et son peuple leur infligèrent une grande défaite, et il tomba d’Israël 500 000 hommes d’élite blessés à mort.
Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
18 Et les fils d’Israël furent humiliés en ce temps-là, et les fils de Juda furent affermis, car ils s’appuyaient sur l’Éternel, le Dieu de leurs pères.
Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
19 Et Abija poursuivit Jéroboam et lui prit des villes: Béthel et les villages de son ressort, et Jeshana et les villages de son ressort, et Éphron et les villages de son ressort.
Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
20 Et Jéroboam n’eut plus de force durant les jours d’Abija; et l’Éternel le frappa, et il mourut.
Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
21 Et Abija s’affermit, et prit 14 femmes, et engendra 22 fils et 16 filles.
Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
22 Et le reste des actes d’Abija, et ses voies et ses paroles, sont écrits dans les commentaires d’Iddo le prophète.
Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.

< 2 Chroniques 13 >