< 1 Samuel 24 >
1 Et il arriva que, quand Saül fut revenu de la poursuite des Philistins, on lui rapporta, en disant: Voici, David est au désert d’En-Guédi.
Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
2 Et Saül prit 3 000 hommes d’élite de tout Israël, et il s’en alla pour chercher David et ses hommes sur les rochers des bouquetins.
Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
3 Et il vint aux parcs du menu bétail, sur le chemin; et là il y avait une caverne, et Saül y entra pour se couvrir les pieds; et David et ses hommes étaient assis au fond de la caverne.
Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
4 Et les hommes de David lui dirent: Voici le jour dont l’Éternel t’a dit: Voici, je livre ton ennemi en ta main, et tu lui feras comme il sera bon à tes yeux. Et David se leva et coupa secrètement le pan de la robe de Saül.
Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
5 Et il arriva, après cela, que le cœur de David le reprit de ce qu’il avait coupé le pan [de la robe] de Saül.
Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
6 Et il dit à ses hommes: Loin de moi, de par l’Éternel, que je fasse une telle chose à mon seigneur, à l’oint de l’Éternel, que d’étendre ma main sur lui; car il est l’oint de l’Éternel.
Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
7 Et David retint ses hommes par ses paroles, et ne leur permit pas de s’élever contre Saül. Et Saül se leva de la caverne, et alla son chemin.
Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
8 Et après cela, David se leva, et sortit de la caverne, et cria après Saül, disant: Ô roi, mon seigneur! Et Saül regarda derrière lui, et David s’inclina le visage contre terre et se prosterna.
Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
9 Et David dit à Saül: Pourquoi écouterais-tu les paroles des hommes qui disent: Voici, David cherche à te faire du mal?
Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
10 Voici, tes yeux ont vu en ce jour que l’Éternel t’a livré aujourd’hui en ma main, dans la caverne. Et on m’a dit de te tuer; et [mon œil] t’a épargné, et j’ai dit: Je n’étendrai point ma main sur mon seigneur, car il est l’oint de l’Éternel.
Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
11 Et regarde, mon père, regarde le pan de ta robe dans ma main; car en ce que j’ai coupé le pan de ta robe et ne t’ai point tué, sache et vois qu’il n’y a pas de mal en ma main, ni de transgression, et que je n’ai pas péché contre toi; et toi, tu fais la chasse à mon âme pour la prendre.
Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
12 L’Éternel jugera entre moi et toi, et l’Éternel me vengera de toi; mais ma main ne sera pas sur toi.
Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
13 Comme dit le proverbe des anciens: Des méchants vient la méchanceté; mais ma main ne sera pas sur toi.
Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
14 Après qui est sorti le roi d’Israël? Qui poursuis-tu? Un chien mort, une puce!
“Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
15 Et l’Éternel sera juge, et il jugera entre moi et toi; et il verra et plaidera ma cause, et me fera droit [en me délivrant] de ta main.
Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
16 Et lorsque David eut achevé de dire ces paroles à Saül, Saül dit: Est-ce là ta voix, mon fils David? Et Saül éleva sa voix et pleura.
Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
17 Et il dit à David: Tu es plus juste que moi, car toi tu m’as rendu le bien, et moi je t’ai rendu le mal;
Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
18 et tu as fait connaître aujourd’hui que tu agissais en bien envers moi, en ce que l’Éternel m’avait livré en ta main, et que tu ne m’as pas tué.
Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
19 Et si un homme a trouvé son ennemi, le laissera-t-il aller sain et sauf? Que l’Éternel te fasse du bien, en récompense de ce que tu as fait aujourd’hui à mon égard!
In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
20 Et maintenant, voici, je sais que certainement tu régneras, et que le royaume d’Israël sera établi en ta main.
Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
21 Et maintenant, jure-moi par l’Éternel que tu ne retrancheras point ma semence après moi, et que tu n’ôteras point mon nom de la maison de mon père.
Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
22 Et David le jura à Saül; et Saül s’en alla dans sa maison; et David et ses hommes montèrent au lieu fort.
Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.