< 1 Rois 5 >

1 Et Hiram, roi de Tyr, envoya ses serviteurs vers Salomon, car il avait entendu qu’on l’avait oint pour roi à la place de son père; car Hiram avait toujours aimé David.
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 Et Salomon envoya vers Hiram, disant:
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 Tu sais, quant à David, mon père, qu’il ne put bâtir une maison pour le nom de l’Éternel, son Dieu, à cause de la guerre dont [ses ennemis] l’entourèrent jusqu’à ce que l’Éternel les mit sous la plante de ses pieds.
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 Mais maintenant l’Éternel, mon Dieu, m’a donné de la tranquillité de tous les côtés; il n’y a ni adversaire ni événement fâcheux.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 Et voici, j’ai résolu de bâtir une maison pour le nom de l’Éternel, mon Dieu, ainsi que l’Éternel a parlé à David, mon père, disant: Ton fils, que je mettrai à ta place sur ton trône, lui, bâtira une maison à mon nom.
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 Et maintenant, commande qu’on me coupe des cèdres dans le Liban; et mes serviteurs seront avec tes serviteurs, et je te donnerai les gages de tes serviteurs selon tout ce que tu [me] diras; car tu sais qu’il n’y a personne parmi nous qui s’entende à couper le bois comme les Sidoniens.
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 Et il arriva, quand Hiram entendit les paroles de Salomon, qu’il s’en réjouit beaucoup; et il dit: Béni soit aujourd’hui l’Éternel, qui a donné à David un fils sage, sur ce grand peuple!
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 Et Hiram envoya à Salomon, disant: J’ai entendu ce que tu m’as envoyé [dire]; je ferai tout ce que tu désires, à l’égard des bois de cèdre et des bois de cyprès.
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 Mes serviteurs les descendront du Liban à la mer, et je les mettrai en radeaux sur la mer [pour les faire passer] jusqu’au lieu que tu m’enverras [dire]; et je les ferai délier là, et tu les enlèveras. Et toi, tu accompliras mon désir, en donnant du pain à ma maison.
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 Et Hiram donna à Salomon des bois de cèdre, et des bois de cyprès, tout ce qu’il désirait;
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 et Salomon donna à Hiram 20 000 cors de froment pour nourrir sa maison, et 20 cors d’huile fine. C’est là ce que Salomon donna à Hiram chaque année.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 Et l’Éternel donna de la sagesse à Salomon, comme il le lui avait dit. Et il y eut paix entre Hiram et Salomon, et ils firent alliance eux deux.
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 Et le roi Salomon fit une levée sur tout Israël, et la levée fut de 30 000 hommes.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 Et il les envoya au Liban, 10 000 par mois, par relais: ils étaient un mois au Liban, deux mois à la maison; et Adoniram était [préposé] sur la levée.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 Et Salomon avait 70 000 [hommes] qui portaient des fardeaux, et 80 000 qui taillaient [la pierre] sur la montagne,
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 outre les chefs, les intendants de Salomon, qui étaient [préposés] sur l’œuvre, 3 300, qui avaient autorité sur le peuple qui travaillait à l’œuvre.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 Et le roi commanda, et on transporta de grandes pierres, des pierres de prix, pour faire les fondements de la maison, des pierres de taille.
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 Et les ouvriers de Salomon et les ouvriers de Hiram, et les Guibliens, taillèrent et préparèrent le bois et les pierres pour bâtir la maison.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.

< 1 Rois 5 >