< 1 Chroniques 20 >

1 Et il arriva, au temps du retour de l’année, au temps où les rois entrent en campagne, que Joab conduisit le gros de l’armée, et dévasta le pays des fils d’Ammon; et il vint et assiégea Rabba; mais David resta à Jérusalem. Et Joab frappa Rabba et la détruisit.
Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
2 Et David prit la couronne de leur roi de dessus sa tête (or elle fut trouvée du poids d’un talent d’or, et il y avait dessus des pierres précieuses); et elle fut [mise] sur la tête de David; et il emmena de la ville une grande quantité de butin.
Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
3 Et il fit sortir le peuple qui s’y trouvait, et les scia avec la scie, et avec des herses de fer, et avec des scies: et David fit ainsi à toutes les villes des fils d’Ammon. Et David et tout le peuple s’en retournèrent à Jérusalem.
ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
4 Et il arriva, après cela, qu’il y eut un combat à Guézer avec les Philistins. Alors Sibbecaï, le Hushathite, frappa Sippaï [qui était] d’entre les enfants du géant; et ils furent subjugués.
Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
5 Et il y eut encore un combat avec les Philistins: et Elkhanan, fils de Jaïr, frappa Lakhmi, frère de Goliath, le Guitthien; et le bois de sa lance était comme l’ensouple des tisserands.
Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
6 Et il y eut encore un combat à Gath: et il y avait [là] un homme de haute stature qui avait six doigts et six [orteils], [en tout] 24; et lui aussi était né au géant.
Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
7 Et il outragea Israël; mais Jonathan, fils de Shimha, frère de David, le frappa.
Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
8 Ceux-là étaient nés au géant, à Gath, et tombèrent par la main de David et par la main de ses serviteurs.
Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.

< 1 Chroniques 20 >