< Psaumes 78 >

1 Cantique d’Asaph. Écoute, ô mon peuple, mon enseignement; prête l’oreille aux paroles de ma bouche.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Je vais ouvrir ma bouche pour dire des sentences, je publierai les mystères des temps anciens.
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 Ce que nous avons entendu, ce que nous avons appris, ce que nos pères nous ont raconté,
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 nous ne le cacherons pas à leurs enfants; nous dirons à la génération future les louanges de Yahweh, et sa puissance, et les prodiges qu’il a opérés.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Il a mis une règle en Jacob, il a établi une loi en Israël, qu’il a enjoint à nos pères d’apprendre à leurs enfants,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 pour qu’elles soient connues des générations suivantes, des enfants qui naîtraient et qui se lèveraient, pour les raconter à leur tour à leurs enfants.
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 Ainsi ils mettraient en Dieu leur confiance, ils n’oublieraient point les œuvres de Dieu, et ils observeraient ses préceptes;
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 ils ne seraient point, comme leurs pères, une race indocile et rebelle, une race au cœur volage, dont l’esprit n’est pas fidèle à Dieu.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Les fils d’Ephraïm, archers habiles à tirer de l’arc, ont tourné le dos au jour du combat;
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 ils n’ont pas gardé l’alliance de Dieu, ils ont refusé de marcher selon sa loi;
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 ils ont mis en oubli ses grandes œuvres, et les merveilles qu’il leur avait montrées.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Devant leurs pères, il avait fait des prodiges, au pays de l’Égypte, dans les campagnes de Tanis.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Il ouvrit la mer pour les faire passer; Il retint les eaux dressées comme un monceau.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Il les conduisit le jour par la nuée, et toute la nuit par un feu brillant.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Il fendit les rochers dans le désert, et il donna à boire comme des flots abondants.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Du rocher il fit jaillir des ruisseaux, et couler l’eau par torrents.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Mais ils continuèrent de pécher contre lui, de se révolter contre le Très-Haut dans le désert.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Ils tentèrent Dieu dans leur cœur, en demandant de la nourriture selon leur convoitise.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Ils parlèrent contre Dieu et dirent: « Dieu pourra-t-il dresser une table dans le désert?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Voici qu’il a frappé le rocher, et des eaux ont coulé, et des torrents se sont répandus; pourra-t-il aussi nous donner du pain ou bien procurer de la viande à son peuple? »
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Yahweh entendit et il fut irrité, un feu s’alluma contre Jacob, et la colère s’éleva contre Israël,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 parce qu’ils n’avaient pas eu foi en Dieu et n’avaient pas espéré en son secours.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Cependant il commanda aux nuées d’en haut, et il ouvrit les portes du ciel;
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 il fit pleuvoir sur eux la manne pour les nourrir, et leur donna le froment du ciel.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Chacun mangea le pain des forts, Il leur envoya de la nourriture à satiété.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Il fit souffler dans le ciel le vent d’orient, il amena par sa puissance le vent du midi;
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 il fit pleuvoir sur eux la viande comme de la poussière, et les oiseaux ailés comme le sable des mers.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Il les fit tomber au milieu de leur camp, autour de leurs tentes.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Ils mangèrent et se rassasièrent à l’excès; Dieu leur donna ce qu’ils avaient désiré.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Ils n’avaient pas encore satisfait leur convoitise, et leur nourriture était encore à leur bouche,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 quand la colère de Dieu s’éleva contre eux; il frappa de mort les mieux repus, il abattit les jeunes hommes d’Israël.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Après tout cela, ils péchèrent encore, et n’eurent pas foi dans ses prodiges.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Alors il dissipa leurs jours comme un souffle, et leurs années par une fin soudaine.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Quand il les frappait de mort, ils le cherchaient, ils revenaient, empressés à retrouver Dieu,
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 ils se rappelaient que Dieu était leur rocher, et le Dieu Très-Haut leur libérateur.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Mais ils le trompaient par leurs paroles, et leur langue lui mentait;
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 leur cœur n’était pas ferme avec lui, ils n’étaient pas fidèles à son alliance.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Mais lui est miséricordieux: il pardonne le péché et ne détruit pas; souvent il retint sa colère, et ne se livra pas à toute sa fureur.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Il se souvenait qu’ils n’étaient que chair, un souffle qui s’en va et ne revient plus.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Que de fois ils se révoltèrent contre lui dans le désert, ils l’irritèrent dans la solitude!
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Ils ne cessèrent de tenter Dieu et de provoquer le Saint d’Israël.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Ils ne se souvinrent plus de sa puissance, du jour où il les délivra de l’oppresseur,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 où il montra ses prodiges en Égypte, ses actions merveilleuses dans les campagnes de Tanis.
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Il changea leurs fleuves en sang, et ils ne purent boire à leurs ruisseaux.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Il envoya contre eux le moucheron qui les dévora, et la grenouille qui les fit périr.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Il livra leurs récoltes à la sauterelle, le produit de leur travail à ses essaims.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Il détruisit leurs vignes par la grêle, et leurs sycomores par les grêlons.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Il abandonna leur bétail à la grêle, et leurs troupeaux aux coups de la foudre.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Il déchaîna contre eux le feu de son courroux, la fureur, la rage et la détresse, toute une armée d’anges de malheur.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Il donna libre carrière à sa colère, il ne sauva pas leur âme de la mort, il livra leur vie à la destruction.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Il frappa tous les premiers-nés en Égypte, les prémices de la force sous les tentes de Cham.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Il fit partir son peuple comme des brebis, il les mena comme un troupeau dans le désert.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Il les dirigea sûrement, sans qu’ils eussent rien à craindre, et la mer engloutit leurs ennemis.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Il les fit arriver jusqu’à sa frontière sainte, jusqu’à la montagne que sa droite a conquise.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Il chassa les nations devant eux, leur assigna par le sort leur part d’héritage, et fit habiter dans leurs tentes les tribus d’Israël.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Cependant ils ont encore tenté et provoqué le Dieu Très-Haut, et ils n’ont pas observé ses ordonnances.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Ils se sont détournés et ont été infidèles comme leurs pères, ils se sont détournés comme un arc trompeur.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Ils l’ont irrité par leurs hauts lieux, ils ont excité sa jalousie par leurs idoles.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Dieu entendit et s’indigna, il prit Israël en grande aversion.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Il dédaigna la demeure de Silo, la tente où il habitait parmi les hommes.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Il livra sa force à la captivité, et sa majesté aux mains de l’ennemi.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Il abandonna son peuple au glaive, et il s’indigna contre son héritage.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Le feu dévora ses jeunes hommes, et ses vierges n’entendirent point le chant nuptial.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Ses prêtres tombèrent par l’épée, et ses veuves ne se lamentèrent point.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Le Seigneur se réveilla, comme un homme endormi, pareil au guerrier subjugué par le vin.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Il frappa ses ennemis par derrière, il leur infligea une honte éternelle.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Mais il prit en aversion la tente de Joseph, et il répudia la tribu d’Ephraïm.
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Il choisit la tribu de Juda, la montagne de Sion qu’il aimait.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Et il bâtit son sanctuaire comme les hauteurs du ciel, comme la terre qu’il a fondée pour toujours.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Il choisit David, son serviteur, et le tira des bergeries;
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 Il le prit derrière les brebis mères, pour paître Jacob, son peuple, et Israël, son héritage.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Et David les guida dans la droiture de son cœur, et il les conduisit d’une main habile.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Psaumes 78 >