< Psaumes 72 >

1 De Salomon. Ô Dieu, donne tes jugements au roi, et ta justice au fils du roi.
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Qu’il dirige ton peuple avec justice, et tes malheureux avec équité!
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Que les montagnes produisent la paix au peuple, ainsi que les collines, par la justice.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Qu’il fasse droit aux malheureux de son peuple, qu’il assiste les enfants du pauvre, et qu’il écrase l’oppresseur!
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 Qu’on te révère, tant que subsistera le soleil, tant que brillera la lune, d’âge en âge!
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Qu’il descende comme la pluie sur le gazon, comme les ondées qui arrosent la terre!
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 Qu’en ses jours le juste fleurisse, avec l’abondance de la paix, jusqu’à ce qu’il n’y ait plus de lune!
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Il dominera d’une mer à l’autre, du Fleuve aux extrémités de la terre.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Devant lui se prosterneront les habitants du désert, et ses ennemis mordront la poussière.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Les rois de Tharsis et des îles paieront des tributs; les rois de Saba et de Méroé offriront des présents.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Tous les rois se prosterneront devant lui; toutes les nations le serviront.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Car il délivrera le pauvre qui crie vers lui, et le malheureux dépourvu de tout secours.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Il aura pitié du misérable et de l’indigent, et il sauvera la vie du pauvre.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Il les affranchira de l’oppression et de la violence, et leur sang aura du prix à ses yeux.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Ils vivront, et lui donneront de l’or de Saba; ils feront sans cesse des vœux pour lui, ils le béniront chaque jour.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Que les blés abondent dans le pays, jusqu’au sommet des montagnes! Que leurs épis s’agitent comme les arbres du Liban! Que les hommes fleurissent dans la ville comme l’herbe des champs!
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Que son nom dure à jamais! Tant que brillera le soleil, que son nom se propage! Qu’on cherche en lui la bénédiction! Que toutes les nations le proclament heureux!
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Béni soit Yahweh Dieu, le Dieu d’Israël, qui seul fait des prodiges!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 Béni soit à jamais son nom glorieux! Que toute la terre soit remplie de sa gloire! Amen! Amen!
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 Fin des prières de David, fils d’Isaï. Psaumes Livres
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Psaumes 72 >