< Psaumes 68 >
1 Au maître de chant. Psaume de David. Cantique. Que Dieu se lève, et que ses ennemis soient dispersés, et que ceux qui le haïssent fuient devant sa face!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 Comme se dissipe la fumée, dissipe- les; comme la cire se fond au feu, que les méchants disparaissent devant Dieu!
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 Mais que les justes se réjouissent et tressaillent devant Dieu; qu’ils soient transportés d’allégresse!
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Chantez à Dieu, célébrez son nom! Frayez le chemin à celui qui s’avance à travers les plaines! Yahweh est son nom; tressaillez devant lui!
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 Il est père des orphelins et juge des veuves, Dieu dans sa sainte demeure.
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 Aux abandonnés Dieu donne une maison; il délivre les captifs et les rend au bonheur; seuls les rebelles restent au désert brûlant.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 Ô Dieu, quand tu sortais à la tête de ton peuple, quand tu t’avançais dans le désert, — Séla.
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 la terre fut ébranlée, les cieux eux-mêmes se fondirent devant Dieu; le Sinaï trembla devant Dieu, le Dieu d’Israël.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 Tu fis tomber, ô Dieu, une pluie de bienfaits; ton héritage était épuisé, tu le réconfortas.
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Envoyés par toi, des animaux vinrent s’y abattre; dans ta bonté, ô Dieu, tu prépares leur aliment aux malheureux.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 Le Seigneur a fait entendre sa parole; les femmes qui annoncent la victoire sont une troupe nombreuse.
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 « Les rois des armées fuient, fuient, et celle qui habite la maison partage le butin. »
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 Quand vous étiez couchés au milieu des bercails, les ailes de la colombe étaient recouvertes d’argent, et ses plumes brillaient de l’éclat de l’or.
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 Lorsque le Tout-Puissant dispersait les rois dans le pays, la neige tombait sur le Selmon.
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 Montagne de Dieu, montagne de Basan, montagne aux cimes élevées, montagne de Basan,
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 pourquoi regardez-vous avec envie, montagnes aux cimes élevées, la montagne que Dieu a voulue pour séjour? Oui, Yahweh y habitera à jamais!
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 Le char de Dieu, ce sont des milliers et des milliers; le Seigneur vient du Sinaï dans son sanctuaire.
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 Tu montes sur la hauteur emmenant la foule des captifs; tu reçois les présents des hommes, Même les rebelles habiteront près de Yahweh Dieu!
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Béni soit le Seigneur! Chaque jour il porte notre fardeau; il est le Dieu qui nous sauve. — Séla.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 Dieu est pour nous le Dieu des délivrances; Yahweh, le Seigneur, peut retirer de la mort.
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 Oui, Dieu brisera la tête de ses ennemis, le front chevelu de celui qui marche dans l’iniquité.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 Le Seigneur a dit: « Je les ramènerai de Basan, je les ramènerai du fond de la mer,
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 afin que tu plonges ton pied dans le sang, et que la langue de tes chiens ait sa part des ennemis. »
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 On voit tes marches, ô Dieu, les marches de mon Dieu, de mon roi, au sanctuaire.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 En avant sont les chanteurs, puis les musiciens, au milieu, des jeunes filles battant du tambourin.
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 « Bénissez Dieu dans les assemblées, le Seigneur, vous qui êtes de la source d’Israël. »
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 Voici Benjamin, le plus petit, qui domine sur eux; voici les princes de Juda avec leur troupe, les princes de Zabulon, les princes de Nephthali.
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 Commande, ô Dieu, à ta puissance, affermis, ô Dieu, ce que tu as fait pour nous.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 À ton sanctuaire, qui s’élève au-dessus de Jérusalem, les rois t’offriront des présents.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Menace la bête des roseaux, la troupe des taureaux avec les veaux des peuples, afin qu’ils se prosternent avec des pièces d’argent. Disperse les nations qui se plaisent aux combats!
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 Que les grands viennent de l’Égypte, que l’Éthiopie s’empresse de tendre les mains vers Dieu.
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 Royaumes de la terre, chantez à Dieu, célébrez le Seigneur! — Séla.
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 Chantez à celui qui est porté sur les cieux, les cieux antiques. Voici qu’il fait entendre sa voix, voix puissante!…
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 Reconnaissez la puissance de Dieu! Sa majesté est sur Israël, et sa puissance est dans les nuées.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 De ton sanctuaire, ô Dieu, tu es redoutable! Le Dieu d’Israël donne à son peuple force et puissance. Béni soit Dieu!
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!