< Psaumes 58 >

1 Au maître de chant. Ne détruis pas. Hymne de David. Est-ce donc en restant muets que vous rendez la justice? Est-ce selon le droit que vous jugez, fils des hommes?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 Non: au fond du cœur vous tramez vos desseins iniques, dans le pays vous vendez au poids la violence de vos mains.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 Les méchants sont pervertis dès le sein maternel, dès leur naissance, les fourbes se sont égarés.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Leur venin est semblable au venin du serpent, de la vipère sourde qui ferme ses oreilles,
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 et n’entend pas la voix de l’enchanteur, du charmeur habile dans son art.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 Ô Dieu brise leurs dents dans leur bouche; Yahweh, arrache les mâchoires des lionceaux!
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 Qu’ils se dissipent comme le torrent qui s’écoule! S’ils ajustent des flèches, qu’elles s’émoussent!
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 Qu’ils soient comme la limace qui va en se fondant! Comme l’avorton d’une femme, qu’ils ne voient point le soleil!
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Avant que vos chaudières sentent l’épine, verte ou enflammée, l’ouragan l’emportera.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 Le juste sera dans la joie, à la vue de la vengeance, il baignera ses pieds dans le sang des méchants.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 Et l’on dira: « Oui, il y a une récompense pour le juste; oui, il y a un Dieu qui juge sur la terre! »
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”

< Psaumes 58 >