< Psaumes 22 >
1 Au maître de chant. Sur « Biche de l’aurore ». Psaume de David. Mon Dieu, mon Dieu, pourquoi m’as-tu abandonné? Je gémis, et le salut reste loin de moi!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Mon Dieu, je crie pendant le jour, et tu ne réponds pas; la nuit, et je n’ai point de repos.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Pourtant tu es saint, tu habites parmi les hymnes d’Israël.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 En toi se sont confiés nos pères; ils se sont confiés, et tu les as délivrés.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Ils ont crié vers toi, et ils ont été sauvés; ils se sont confiés en toi, et ils n’ont pas été confus.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Et moi, je suis un ver, et non un homme, l’opprobre des hommes et le rebut du peuple.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Tous ceux qui me voient se moquent de moi; ils ouvrent les lèvres, ils branlent la tête:
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 « Qu’il s’abandonne à Yahweh! Qu’il le sauve, qu’il le délivre, puisqu’il l’aime! »
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Oui, c’est toi qui m’as tiré du sein maternel, qui m’as donné confiance sur les mamelles de ma mère.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 Dès ma naissance, je t’ai été abandonné; depuis le sein de ma mère, c’est toi qui es mon Dieu.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Ne t’éloigne pas de moi, car l’angoisse est proche, car personne ne vient à mon secours.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Autour de moi sont de nombreux taureaux, les forts de Basan m’environnent.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Ils ouvrent contre moi leur gueule, comme un lion qui déchire et rugit.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Je suis comme de l’eau qui s’écoule, et tous mes os sont disjoints; mon cœur est comme de la cire, il se fond dans mes entrailles.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Ma force s’est desséchée comme un tesson d’argile, et ma langue s’attache à mon palais; tu me couches dans la poussière de la mort.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Car des chiens m’environnent, une troupe de scélérats rôdent autour de moi; ils ont percé mes pieds et mes mains,
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 je pourrais compter tous mes os. Eux, ils m’observent, ils me contemplent;
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 ils se partagent mes vêtements, ils tirent au sort ma tunique.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Et toi, Yahweh, ne t’éloigne pas! Toi qui es ma force, viens en hâte à mon secours!
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Délivre mon âme de l’épée, ma vie du pouvoir du chien!
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Sauve-moi de la gueule du lion, tire-moi des cornes du buffle!
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 Alors j’annoncerai ton nom à mes frères, au milieu de l’assemblée je te louerai:
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 « Vous qui craignez Yahweh, louez-le! Vous tous, postérité de Jacob, glorifiez-le! Révérez-le, vous tous, postérité d’Israël!
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Car il n’a pas méprisé, il n’a pas rejeté la souffrance de l’affligé, il n’a pas caché sa face devant lui, et quand l’affligé a crié vers lui, il a entendu. »
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 Grâce à toi, mon hymne retentira dans la grande assemblée, j’acquitterai mes vœux en présence de ceux qui te craignent.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Les affligés mangeront et se rassasieront; ceux qui cherchent Yahweh le loueront. Que votre cœur revive à jamais!
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Toutes les extrémités de la terre se souviendront et se tourneront vers Yahweh, et toutes les familles des nations se prosterneront devant sa face.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Car à Yahweh appartient l’empire, il domine sur les nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Les puissants de la terre mangeront et se prosterneront; devant lui s’inclineront tous ceux qui descendent à la poussière, ceux qui ne peuvent prolonger leur vie.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 La postérité le servira; on parlera du Seigneur à la génération future.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 Ils viendront et ils annonceront sa justice, au peuple qui naîtra, ils diront ce qu’il a fait.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.