< Psaumes 130 >
1 Cantique des montées. Du fond de l’abîme je crie vers toi, Yahweh.
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Seigneur, écoute ma voix; que tes oreilles soient attentives aux accents de ma prière!
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Si tu gardes le souvenir de l’iniquité, Yahweh, Seigneur, qui pourra subsister?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Mais auprès de toi est le pardon, afin qu’on te révère.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 J’espère en Yahweh; mon âme espère, et j’attends sa parole.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 Mon âme aspire après le Seigneur plus que les guetteurs n’aspirent après l’aurore.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Israël, mets ton espoir en Yahweh! Car avec Yahweh est la miséricorde, avec lui une surabondante délivrance.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 C’est lui qui rachètera Israël de toutes ses iniquités.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.