< Psaumes 110 >
1 Psaume de David. Yahweh a dit à mon Seigneur: « Assieds-toi à ma droite, jusqu’à ce que je fasse de tes ennemis l’escabeau de tes pieds. »
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 Yahweh étendra de Sion le sceptre de ta puissance: Règne en maître au milieu de tes ennemis!
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 Ton peuple accourt à toi au jour où tu rassembles ton armée, avec des ornements sacrés; du sein de l’aurore vient à toi la rosée de tes jeunes guerriers.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 Le Seigneur l’a juré, il ne s’en repentira point: « Tu es prêtre pour toujours à la manière de Melchisédech. »
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 Le Seigneur, est à droite, Il brisera les rois au jour de sa colère.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 Il exerce son jugement parmi les nations: tout est rempli de cadavres; il brise les têtes de la terre entière.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 Il boit au torrent sur le chemin, c’est pourquoi il relève la tête.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.