< Psaumes 11 >
1 Au maître de chant. De David. En Yahweh je me confie; comment dites-vous à mon âme: « Fuyez à votre montagne, comme l’oiseau.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
2 Car voici que les méchants bandent l’arc, ils ont ajusté leur flèche sur la corde, pour tirer dans l’ombre sur les hommes au cœur droit.
Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
3 Quand les fondements sont renversés, que peut faire le juste? »
Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
4 Yahweh dans son saint temple, Yahweh, qui a son trône dans les cieux, a les yeux ouverts; ses paupières sondent les enfants des hommes.
Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
5 Yahweh sonde le juste; il hait le méchant et celui qui se plaît à la violence.
Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
6 Il fera pleuvoir sur les méchants des lacets, du feu et du soufre; un vent brûlant, voilà la coupe qu’ils auront en partage.
A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
7 Car Yahweh est juste, il aime la justice; les hommes droits contempleront sa face.
Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.