< Psaumes 107 >
1 Célébrez Yahweh, car il est bon, car sa miséricorde est éternelle.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qu’ ainsi disent les rachetés de Yahweh, ceux qu’il a rachetés des mains de l’ennemi,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 et qu’il a rassemblés de tous les pays, de l’orient et de l’occident, du nord et de la mer!
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Ils erraient dans le désert, dans un chemin solitaire, sans trouver une ville à habiter.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 En proie à la faim, à la soif, ils sentaient leur âme défaillir.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Dans leur détresse, ils crièrent vers Yahweh, et il les délivra de leurs angoisses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Il les mena par le droit chemin, pour les faire arriver à une ville habitable.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Qu’ils louent Yahweh pour sa bonté, et pour ses merveilles en faveur du fils de l’homme.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Car il a désaltéré l’âme altérée, et comblé de biens l’âme affamée.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Ils habitaient les ténèbres et l’ombre de la mort, prisonniers dans la souffrance et dans les fers.
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Parce qu’ils s’étaient révoltés contre les oracles de Dieu, et qu’ils avaient méprisé le conseil du Très-Haut,
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 il humilia leur cœur par la souffrance; ils s’affaissèrent, et personne ne les secourut.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Dans leur détresse, ils crièrent vers Yahweh, et il les sauva de leurs angoisses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Il les tira des ténèbres et de l’ombre de la mort, et il brisa leurs chaînes.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Qu’ils louent Yahweh pour sa bonté, et pour ses merveilles en faveur des fils de l’homme.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Car il a brisé les portes d’airain et mis en pièces les verrous de fer.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Les insensés! par leur conduite criminelle, et par leurs iniquités, ils avaient attiré sur eux la souffrance.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Leur âme avait en horreur toute nourriture, et ils touchaient aux portes de la mort.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Dans leur détresse, ils crièrent vers Yahweh, et il les sauva de leurs angoisses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Il envoya sa parole et il les guérit, et il les fit échapper de leurs tombeaux.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Qu’ils louent Yahweh pour sa bonté, et pour ses merveilles en faveur des fils de l’homme!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Qu’ils offrent des sacrifices d’actions de grâce, et qu’ils publient ses œuvres avec des cris de joie!
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Ils étaient descendus sur la mer dans des navires, pour faire le négoce sur les vastes eaux:
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 — ceux là ont vu les œuvres de Yahweh, et ses merveilles au milieu de l’abîme —
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Il dit, et il fit lever un vent de tempête, qui souleva les flots de la mer.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Ils montaient jusqu’aux cieux, ils descendaient dans les abîmes; leur âme défaillait dans la peine.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Saisis de vertige, ils chancelaient comme un homme ivre, et toute leur sagesse était anéantie.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Dans leur détresse, ils crièrent vers Yahweh, et il les tira de leurs angoisses.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Il changea l’ouragan en brise légère, et les vagues de la mer se turent.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Ils se réjouirent en les voyant apaisées, et Yahweh les conduisit au port désiré.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Qu’ils louent Yahweh pour sa bonté, et pour ses merveilles en faveur des fils de l’homme!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Qu’ils l’exaltent dans l’assemblée du peuple, et qu’ils le célèbrent dans le conseil des anciens!
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Il a changé les fleuves en désert, et les sources d’eau en sol aride;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Le pays fertile en plaine de sel, à cause de la méchanceté de ses habitants.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Il a fait du désert un bassin d’eau, et de la terre aride un sol plein de sources.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Il y établit les affamés, et ils fondèrent une ville pour l’habiter.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Ils ensemencèrent des champs, et ils plantèrent des vignes, et ils recueillirent d’abondantes récoltes.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Il les bénit, et ils se multiplièrent beaucoup, et il ne laissa pas diminuer leurs troupeaux.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Ils avaient été réduits à un petit nombre et humiliés, sous l’accablement du malheur et de la souffrance.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Il avait répandu la honte sur leurs princes, il les avait fait errer dans des déserts sans chemins.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Mais il a relevé le malheureux de la misère, et il a rendu les familles pareilles à des troupeaux.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Les hommes droits le voient et se réjouissent, et tous les méchants ferment la bouche.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Que celui qui est sage prenne garde à ces choses, et qu’il comprenne les bontés de Yahweh!
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.