< Psaumes 102 >
1 Prière du malheureux, lorsqu’il est accablé et qu’il répand sa plainte devant Yahweh. Yahweh écoute ma prière, et que mon cri arrive jusqu’à toi.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Ne me cache pas ton visage, au jour de ma détresse; incline vers moi ton oreille, quand je crie, hâte-toi de m’exaucer.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Car mes jours s’évanouissent comme en fumée, et mes os sont embrasés comme par un feu.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Frappé comme l’herbe, mon cœur se dessèche; j’oublie même de manger mon pain.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 À force de crier et de gémir, mes os s’attachent à ma chair.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Je ressemble au pélican du désert, je suis devenu comme le hibou des ruines.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Je passe les nuits sans sommeil, comme l’oiseau solitaire sur le toit.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Tout le jour mes adversaires m’outragent, mes ennemis furieux jurent ma ruine.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Je mange la cendre comme du pain, et je mêle mes larmes à mon breuvage,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 à cause de ta colère et de ton indignation, car tu m’as soulevé et jeté au loin.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Mes jours sont comme l’ombre qui s’allonge, et je me dessèche comme l’herbe.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Mais toi, Yahweh, tu es assis sur un trône éternel, et ta mémoire vit d’âge en âge.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Tu te lèveras, tu auras pitié de Sion, car le temps de lui faire grâce, le moment fixé est venu.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Car tes serviteurs en chérissent les pierres, ils s’attendrissent sur sa poussière.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Alors les nations révéreront le nom de Yahweh, et tous les rois de la terre ta majesté,
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 parce que Yahweh a rebâti Sion; il s’est montré dans sa gloire.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Il s’est tourné vers la prière du misérable, il n’a pas dédaigné sa supplication.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Que cela soit écrit pour la génération future, et que le peuple qui sera créé célèbre Yahweh,
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 parce qu’il a regardé de sa sainte hauteur, parce que Yahweh a regardé des cieux sur la terre,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 pour écouter les gémissements des captifs, pour délivrer ceux qui sont voués à la mort,
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 afin qu’ils publient dans Sion le nom de Yahweh, et sa louange dans Jérusalem,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 quand s’assembleront tous les peuples, et les royaumes pour servir Yahweh.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Il a brisé ma force sur le chemin, il a abrégé mes jours.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Je dis: Mon Dieu, ne m’enlève pas au milieu de mes jours, toi, dont les années durent d’âge en âge.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Au commencement tu as fondé la terre, et les cieux sont l’ouvrage de tes mains.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Ils périront, mais toi, tu subsistes. Tu les changeras comme un manteau, et ils seront changés:
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 mais toi, tu restes le même, et tes années n’ont point de fin.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Les fils de tes serviteurs habiteront leur pays, et leur postérité sera stable devant toi.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”