< Proverbes 7 >

1 Mon fils, retiens mes paroles, et garde avec toi mes préceptes.
Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
2 Observe mes préceptes, et tu vivras, garde mon enseignement comme la prunelle de tes yeux.
Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
3 Lie-les sur tes doigts, écris-les sur la table de ton cœur.
Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Dis à la sagesse: Tu es ma sœur! et appelle l’intelligence ton amie,
Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
5 pour qu’elle te préserve de la femme d’autrui, de l’étrangère qui fait entendre de douces paroles.
za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
6 Étant à la fenêtre de ma maison, je regardais à travers le treillis.
A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
7 J’aperçus parmi les insensés, je remarquai parmi les jeunes gens un garçon dépourvu de sens.
Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
8 Il passait dans la rue, près du logis d’ une étrangère, et il s’avançait vers sa demeure.
Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
9 C’était au crépuscule, à la chute du jour, au milieu de la nuit et de l’obscurité.
da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
10 Et voilà qu’une femme l’aborde, ayant la mise d’une courtisane et la dissimulation dans le cœur.
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
11 Elle est impétueuse et indomptable; ses pieds ne peuvent se reposer dans sa maison;
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
12 tantôt dans la rue, tantôt sur les places, et près de tous les angles, elle se tient aux aguets.
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
13 Elle saisit le jeune homme et l’embrasse, et avec un visage effronté lui dit:
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
14 « Je devais offrir des victimes pacifiques, aujourd’hui j’ai accompli mes vœux.
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
15 C’est pourquoi je suis sortie à ta rencontre, pour te chercher, et je t’ai trouvé.
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
16 J’ai garni mon lit de couvertures, de tapis de fil d’Égypte.
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
17 J’ai parfumé ma couche de myrrhe, d’aloès et de cinnamome.
Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
18 Viens, enivrons-nous d’amour jusqu’au matin, livrons-nous aux délices de la volupté.
Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
19 Car mon mari n’est pas à la maison, il est parti pour un lointain voyage;
Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
20 il a pris avec lui le sac de l’argent, il ne reviendra à la maison qu’à la pleine lune. »
Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
21 Elle le séduit à force de paroles, elle l’entraîne par les paroles de ses lèvres;
Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
22 il se met aussitôt à la suivre, comme le bœuf qui va à la boucherie, comme l’insensé qui court au châtiment des entraves,
Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
23 jusqu’à ce qu’une flèche lui perce le foie, comme l’oiseau qui se précipite dans le filet, sans savoir qu’il y va pour lui de sa vie.
sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
24 Et maintenant, mes fils, écoutez-moi, et soyez attentifs aux paroles de ma bouche.
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
25 Que ton cœur ne se détourne pas vers ses voies, ne t’égare pas dans ses sentiers.
Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
26 Car elle a fait de nombreux blessés, et nombreuses ont été ses victimes.
Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
27 Sa maison est le chemin du schéol, qui descend au séjour de la mort. (Sheol h7585)
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)

< Proverbes 7 >