< Nombres 27 >

1 Alors s'approchèrent les filles de Salphaad, fils de Hépher, fils de Galaad, fils de Machir, fils de Manassé, des familles de Manassé, le fils de Joseph; leurs noms étaient Maala, Noa, Hégla, Melcha et Thersa.
’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
2 Elles se présentèrent devant Moïse, devant le prêtre Eléazar, et devant les princes de toute l'assemblée, à l'entrée de la tente de réunion, et elles dirent:
Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
3 « Notre père est mort dans le désert; il n'était pas au milieu de la troupe de ceux qui se liguèrent contre Yahweh, de la troupe de Coré, mais il est mort pour son péché, et il n'avait point de fils.
“Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
4 Pourquoi le nom de notre père serait-il retranché du milieu de sa famille, parce qu'il n'a pas eu de fils? Donne-nous une propriété parmi les frères de notre père. »
Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
5 Moïse porta leur cause devant Yahweh;
Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
6 et Yahweh dit à Moïse:
Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
7 « Les filles de Salphaad ont dit une chose juste. Tu leur donneras en héritage une propriété parmi les frères de leur père, et tu leur feras passer l'héritage de leur père.
“Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
8 Tu parleras aux enfants d'Israël, en disant: Si un homme meurt sans avoir de fils, vous ferez passer son héritage à sa fille;
“Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
9 et s'il n'a point de fille, vous donnerez son héritage à ses frères.
In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
10 S'il n'a point de frères, vous donnerez son héritage aux frères de son père;
In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
11 et s'il n'y a point de frères de son père, vous donnerez son héritage au parent le plus proche dans sa famille, et c'est lui qui le possédera. Ce sera pour les enfants d'Israël une règle de droit, comme Yahweh l'a ordonné à Moïse. »
In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
12 Yahweh dit à Moïse: « Monte sur cette montagne d'Abarim, et vois le pays que je donne aux enfants d'Israël.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
13 Tu le verras, et toi aussi tu seras recueilli auprès de ton peuple, comme Aaron, ton frère, a été recueilli,
Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
14 parce que dans le désert de Sin, lors de la contestation de l'assemblée, vous avez été tous deux rebelles à l'ordre que j'avais donné de me sanctifier devant eux à l'occasion des eaux. Ce sont les eaux de Mériba, à Cadès, dans le désert de Sin. »
gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
15 Moïse parla à Yahweh, en disant:
Musa ya ce wa Ubangiji,
16 « Que Yahweh, le Dieu des esprits de toute chair, établisse sur l'assemblée un homme
“Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
17 qui sorte devant eux et qui entre devant eux, qui les fasse sortir et qui les fasse entrer, afin que l'assemblée de Yahweh ne soit pas comme des brebis qui n'ont point de berger. »
yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
18 Yahweh dit à Moïse: « Prends Josué, fils de Nun, homme en qui réside l'Esprit, et tu poseras ta main sur lui.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
19 Tu le placeras devant Eléazar, le prêtre, et devant toute l'assemblée, et tu l'installeras sous leurs yeux.
Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
20 Tu mettras sur lui une part de ton autorité, afin que toute l'assemblée des enfants d'Israël lui obéisse.
Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
21 Il se présentera devant le prêtre Eléazar, qui consultera pour lui le jugement de l'Urim devant Yahweh; c'est sur son ordre que sortiront, sur son ordre qu'entreront, lui, Josué, tous les enfants d'Israël avec lui et toute l'assemblée. »
Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
22 Moïse fit ce que Yahweh lui avait ordonné. Il prit Josué, et il le plaça devant Eléazar, le prêtre, et devant toute l'assemblée.
Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
23 Et ayant posé ses mains sur lui, il l'installa, comme Yahweh l'avait dit par Moïse.
Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.

< Nombres 27 >