< Luc 10 >

1 Après cela, le Seigneur en désigna encore soixante-douze autres, et les envoya devant lui, deux à deux, dans toutes les villes et tous les lieux où lui-même devait aller.
Bayan wadannan abubuwa, Ubangiji ya sake nada wadansu saba'in ya aike su biyu biyu, domin su tafi kowanne birni da wurin da yake niyyan zuwa.
2 Il leur dit: « La moisson est grande, mais les ouvriers sont en petit nombre. Priez donc le maître de la moisson d’envoyer des ouvriers à sa moisson.
Ya ce da su, “Girbin yana da yawa, amma ma'aikatan sun yi kadan. Saboda haka kuyi addu'a sosai ga Ubangijin girbin, domin ya aiko da ma'aikata cikin gonarsa.
3 Partez: voici que je vous envoie comme des agneaux au milieu des loups.
Ku tafi, duba na aike ku kamar 'yan raguna cikin kyarkyetai.
4 Ne portez ni bourse, ni sac, ni souliers, et ne saluez personne en chemin.
Kada ku dauki jakan kudi, ko jakar matafiyi, ko takalma, kada ku gai da kowa a kan hanya.
5 Dans quelque maison que vous entriez, dites d’abord: Paix à cette maison!
Dukan gidan da ku ka shiga, ku fara cewa, 'Bari salama ta kasance a wannan gida.'
6 Et s’il s’y trouve un enfant de paix, votre paix reposera sur lui; sinon, elle reviendra à vous.
Idan akwai mutum mai salama a gidan, salamar ku za ta kasance a kansa, amma idan babu, salamar ku za ta dawo wurinku.
7 Demeurez dans la même maison, mangeant et buvant de ce qu’il y aura chez eux; car l’ouvrier mérite son salaire. Ne passez pas d’une maison dans une autre.
Ku zauna a wannan gidan, ku ci ku sha abin da suka tanada maku. Gama ma'aikaci ya wajibci ladansa. Kada ku bi gida gida.
8 Dans quelque ville que vous entriez, si l’on vous reçoit, mangez ce qu’on vous présentera;
Dukan birnin da ku ka shiga kuma sun karbe ku, ku ci abin da suka sa a gabanku.
9 guérissez les malades qui s’y trouveront, et dites-leur: Le royaume de Dieu est proche de vous.
Ku warkar da marasa lafiyar da ke wurin. Ku ce da su, 'Mulkin Allah ya zo kusa da ku.'
10 Mais dans quelque ville que vous entriez, si l’on ne vous reçoit pas, allez sur les places publiques et dites:
Amma dukan birnin da ku ka shiga, idan ba su karbe ku ba, ku tafi cikin titunansu, ku ce,
11 La poussière même de votre ville, qui s’est attachée à nous, nous l’essuyons contre vous; sachez cependant ceci, c’est que le royaume de Dieu est proche.
'Ko kurar birninku da ta like a kafafunmu, mun karkabe maku ita a matsayin shaida a kanku! Amma ku sani mulkin Allah ya zo kusa da ku.'
12 Je vous le dis, il y aura, en ce jour-là, moins de rigueur pour Sodome que pour cette ville.
Na gaya maku, a ranar shari'a Saduma za ta fi wannan birni samun sauki.
13 Malheur à toi, Corozaïn! Malheur à toi, Bethsaïde! Car si les miracles qui ont été faits au milieu de vous, l’avaient été dans Tyr et dans Sidon, elles auraient depuis longtemps fait pénitence, assises sous le cilice et la cendre.
Kaiton ki, Korasinu! Kaiton ki, Baitsaida! Ayyuka masu girma da aka yi a cikinku, da an yi su a cikin Taya da Sidon, da sun tuba tuntuni a zaune cikin toka da tufafin makoki.
14 C’est pourquoi, il y aura, au jugement, moins de rigueur pour Tyr et pour Sidon que pour vous.
Amma a ranar shari'a Taya da Sidon za su fi ku samun sauki.
15 Et toi, Capharnaüm, qui t’élèves au ciel, tu seras abaissée jusqu’aux enfers. (Hadēs g86)
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani har zuwa sama za a daukaka ki? Babu, za a gangarar dake har zuwa hadas. (Hadēs g86)
16 Celui qui vous écoute, m’écoute, et celui qui vous méprise, me méprise; or celui qui me méprise, méprise Celui qui m’a envoyé. »
Wanda ya saurare ku ya saurare ni, wanda ya ki ku, ya ki ni, kuma wanda ya ki ni, ya ki wanda ya aiko ni.”
17 Les soixante-douze revinrent avec joie, disant: « Seigneur, les démons mêmes nous sont soumis en votre nom. »
Su saba'in din suka dawo da murna, suna cewa, “Ubangiji, har ma aljanu suna yi mana biyayya, a cikin sunanka.”
18 Il leur répondit: « Je contemplais Satan tombant du ciel comme la foudre.
Sai Yesu ya ce masu, “Na ga Shaidan yana fadowa daga sama kamar walkiya.
19 Voilà que je vous ai donné le pouvoir de fouler aux pieds les serpents et les scorpions, et toute la puissance de l’ennemi, et elle ne pourra vous nuire en rien.
Duba, na ba ku iko ku taka macizai da kunamai, da kuma kan dukan ikon magabci, kuma ba zai iya yin illa a gareku ba ko kadan.
20 Seulement ne vous réjouissez pas de ce que les esprits vous sont soumis; mais réjouissez-vous de ce que vos noms sont écrits dans les cieux. »
Amma duk da haka kada ku yi murna a kan wannan kadai cewa ruhohi suna yi maku biyayya, amma ku yi murna domin an rubuta sunayenku a cikin sama.”
21 Au même moment, il tressaillit de joie sous l’action de l’Esprit-Saint, et il dit: « Je vous bénis, ô Père, Seigneur du ciel et de la terre, de ce que vous avez caché ces choses aux sages et aux prudents, et les avez révélées aux petits enfants. Oui, je vous bénis, ô Père, de ce qu’il vous a plu ainsi.
Cikin wannan lokacin, ya yi farin ciki kwarai cikin Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Na ba ka girma, ya Uba, Ubangijin sama da kasa. Domin ka rufe wadannan abubuwa daga masu hikima da ganewa, ka bayyana su ga wadanda ba koyayyu ba ne, kamar kananan yara. I, Uba gama haka ne ya gamshe ka.”
22 Toutes choses m’ont été données par mon Père; et personne ne sait ce qu’est le Fils, si ce n’est le Père, et ce qu’est le Père, si ce n’est le Fils, et celui à qui le Fils veut bien le révéler. »
Dukan abu, Ubana ya damka su gare ni, kuma babu wanda ya san Dan, sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Dan. Sai kuma wanda Dan ya yi niyyar ya bayyana Uban a gareshi.”
23 Et se tournant vers ses disciples, il leur dit en particulier: « Heureux les yeux qui voient ce que vous voyez!
Ya juya wajen almajiran, ya ce da su a kadaice, “Masu albarka ne su wadanda suka ga abin da kuke gani.
24 Car, je vous le dis, beaucoup de prophètes et de rois ont désiré voir ce que vous voyez, et ne l’ont pas vu, entendre ce que vous entendez, et ne l’ont pas entendu. »
Na fada maku, annabawa da yawa, da sarakuna da yawa sun so da sun ga abubuwan da kuke gani, amma ba su gani ba. Kuma sun so da sun ji abubuwan da kuke ji, amma ba su ji su ba.”
25 Et voici qu’un docteur de la Loi, s’étant levé, lui dit pour l’éprouver: « Maître, que ferai-je pour posséder la vie éternelle? » (aiōnios g166)
Sai ga wani malamin shari'ar Yahudawa, ya zo ya gwada shi da cewa, “Malam, me zan yi domin in gaji rai na har abada?” (aiōnios g166)
26 Jésus lui dit: « Qu’y a-t-il d’écrit dans la Loi? Qu’y lis-tu? »
Sai Yesu ya ce masa, “Yaya kake karanta abin da aka rubuta cikin shari'a?”
27 Il répondit: « Tu aimeras le Seigneur ton Dieu de tout cœur, de toute ton âme, de toute tes forces et de tout ton esprit, et ton prochain comme toi-même. »
Ya amsa ya ce,”Dole ne ka kaunaci Ubangiji Allah da dukan zuciyarka, da dukan ranka da dukan karfinka, da dukan lamirinka. Ka kuma kaunaci makwabcinka kamar kanka.”
28 Jésus lui dit: « Tu as bien répondu, fais cela et tu vivras. »
Yesu ya ce ma sa, “Ka amsa daidai, idan ka yi haka za ka rayu.”
29 Mais cet homme, voulant se justifier, dit à Jésus: « Et qui est mon prochain? »
Amma, malamin ya na so ya 'yantar da kansa, sai ya ce da Yesu, “To, wanene makwabcina?”
30 Jésus reprit: « Un homme descendait de Jérusalem à Jéricho; il tomba entre les mains des brigands, qui le dépouillèrent, et l’ayant chargé de coups, se retirèrent, le laissant à demi-mort.
Ya amsa ya ce, “Wani mutum yana tafiya daga Urushalima za shi Yariko. Sai ya fada hannun mafasa, suka tube shi, suka kwace dukan abin da ya ke da shi, suka yi masa duka, suka bar shi kamar matacce.
31 Or, il arriva qu’un prêtre descendait par le même chemin; il vit cet homme et passa outre.
Ya zama sai ga wani firist ya na bin wannan hanya, da ya gan shi sai ya bi ta gefe daya ya wuce.
32 De même un lévite, étant venu dans ce lieu, s’approcha, le vit et passa outre.
Haka kuma sai ga wani Balawi, sa'adda ya zo wurin, ya gan shi sai ya bi ta wani gefe ya wuce shi.
33 Mais un Samaritain, qui était en voyage, arriva près de lui, et, le voyant, fut touché de compassion.
Amma wani Basamariye, ya na tafiya sa'adda ya zo wurin da mutumin yake, sa'adda ya ga mutumin sai tausayi ya kama shi.
34 Il s’approcha, banda ses plaies, après y avoir versé de l’huile et du vin; puis il le mit sur sa propre monture, le mena dans une hôtellerie, et prit soin de lui.
Ya zo inda mutumin yake, ya daure masa raunukan da aka ji masa, yana shafa masu mai da ruwan inabi. Ya dora shi a kan dabbarsa ya kawo shi wurin kwana, ya kula da shi
35 Le lendemain, tirant deux deniers, il les donna à l’hôte et lui dit: Aie soin de cet homme, et tout ce que tu dépenseras de plus, je te le rendrai à mon retour.
Washegari ya kawo dinari biyu, ya ba mai wurin kwanan ya ce 'Ka kula da shi, idan ma ka kashe fiye da haka, idan na dawo zan biya ka.'
36 Lequel de ces trois te semble avoir été le prochain de l’homme qui tomba entre les mains des brigands? »
A cikinsu ukun nan, wanene kake tsammani makwabcin wannan mutum da ya fada hannun 'yan fashi?”
37 Le docteur répondit: « Celui qui a pratiqué la miséricorde envers lui. » Et Jésus lui dit: « Toi aussi, va et fais de même. »
Sai malamin ya ce, “Wannan da ya nuna masa jinkai” Sai Yesu yace masa, “Ka je kai ma ka yi haka.”
38 Pendant qu’ils étaient en chemin, Jésus entra dans un village, et une femme, nommée Marthe, le reçut dans sa maison.
Sa'adda suke tafiya, sai ya shiga cikin wani kauye, sai wata mata mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
39 Elle avait une sœur, nommée Marie, qui, s’étant assise aux pieds du Seigneur, écoutait sa parole,
Tana da 'yar'uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a kafafun Ubangiji tana jin abin da yake fadi.
40 tandis que Marthe s’empressait aux divers soins du service. S’étant donc arrêtée: « Seigneur, dit-elle, ne vous mettez-vous pas en peine que ma sœur m’ait laissée servir seule? Dites-lui donc de m’aider. »
Amma ita Marta ta na ta kokari ta shirya abinci. Sai ta zo wurin Yesu ta ce, “Ubangiji, ba ka damu ba 'yar'uwata ta bar ni ina ta yin aiki ni kadai? Ka ce da ita ta taya ni.”
41 Le Seigneur lui répondit: « Marthe, Marthe, vous vous inquiétez et vous agitez pour beaucoup de choses.
Amma Ubangiji ya amsa ya ce da ita, “Marta, Marta, kin damu a kan abubuwa da yawa,
42 Une seule est nécessaire. Marie a choisi la bonne part, qui ne lui sera point ôtée. »
amma abu daya ne ya zama dole. Maryamu ta zabi abu mafi kyau, wanda ba za a iya kwace mata ba.”

< Luc 10 >