< Lévitique 24 >
1 Yahweh parla à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 « Ordonne aux enfants d’Israël de t’apporter pour le chandelier de l’huile pure d’olives concassées, pour entretenir les lampes continuellement.
“Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
3 En dehors du voile qui est devant le témoignage, dans la tente de réunion, Aaron la préparera pour brûler continuellement du soir au matin en présence de Yahweh. C’est une loi perpétuelle pour vos descendants.
Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
4 Il arrangera les lampes sur le chandelier d’or pur, pour qu’elles brûlent constamment devant Yahweh.
Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
5 « Tu prendras de la fleur de farine, et tu en cuiras douze gâteaux; chaque gâteau sera de deux dixièmes d’épha.
“Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
6 Tu les placeras en deux piles, six par pile, sur la table d’or pur devant Yahweh.
A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
7 Tu mettras de l’encens pur sur chaque pile, et il servira, pour le pain, de mémorial offert par le feu à Yahweh.
Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
8 Chaque jour de sabbat, on disposera ces pains devant Yahweh constamment, de la part des enfants d’Israël: c’est une alliance perpétuelle.
Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
9 Ils appartiendront à Aaron et à ses fils, qui les mangeront en lieu saint; car c’est pour eux une chose très sainte parmi les offrandes faites par le feu à Yahweh. C’est une loi perpétuelle. »
Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
10 Le fils d’une femme israélite, mais qui était fils d’un Égyptien, vint au milieu des enfants d’Israël, et il y eut une querelle dans le camp entre le fils de la femme israélite et un homme d’Israël.
To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
11 Le fils de la femme israélite blasphéma le Nom sacré et le maudit, et sa mère s’appelait Salumith, fille de Dabri, de la tribu de Dan.
Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
12 On le mit sous garde, pour que Moïse leur déclarât de la part de Yahweh, ce qu’il y avait à faire.
Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
13 Yahweh parla à Moïse, en disant:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
14 « Fais sortir du camp le blasphémateur; que tous ceux qui l’ont entendu posent leurs mains sur sa tête, et que toute l’assemblée le lapide.
“Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
15 Tu parleras aux enfants d’Israël, en disant: Tout homme qui maudit son Dieu portera son péché;
Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
16 et celui qui blasphémera le nom de Yahweh sera puni de mort: toute l’assemblée le lapidera. Étranger ou indigène, s’il blasphème le Nom sacré, il mourra.
duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
17 Celui qui frappe un homme mortellement sera mis à mort.
“‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
18 Celui qui frappe mortellement une tête de bétail en donnera une autre: vie pour vie.
Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
19 Si quelqu’un fait une blessure à son prochain, on lui fera comme il a fait:
Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
20 fracture pour fracture, œil pour œil, dent pour dent; on lui fera la même blessure qu’il a faite à son prochain.
karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
21 Celui qui aura tué une pièce de bétail en rendra une autre; mais celui qui aura tué un homme sera mis à mort.
Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
22 La même loi régnera parmi vous, pour l’étranger comme pour l’indigène; car je suis Yahweh, votre Dieu ».
Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
23 Moïse ayant ainsi parlé aux enfants d’Israël, ils firent sortir du camp le blasphémateur, et le lapidèrent. Les enfants d’Israël firent selon que Yahweh avait ordonné à Moïse.
Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.