< Josué 16 >
1 La part échue par le sort aux fils de Joseph commençait, du côté de l’orient, depuis le Jourdain de Jéricho, jusqu’aux eaux de Jéricho; c’était ensuite le désert qui monte de Jéricho à Béthel par la montagne.
Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
2 La frontière aboutissait de Béthel à Luz, et passait vers la frontière des Archéens à Ataroth.
Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
3 De là, elle descendait à l’occident, vers la frontière des Jephlétiens jusqu’à la frontière de Béthoron le Bas et jusqu’à Gazer, et elle aboutissait à la mer.
ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
4 Tel est l’héritage que reçurent les fils de Joseph, Manassé et Ephraïm.
Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
5 Voici la frontière des fils d’Ephraïm, selon leurs familles. La limite de leur héritage était, à l’orient, Ataroth-Addar jusqu’à Béthoron le Haut.
Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
6 La frontière aboutissait, du côté de l’occident, vers Machméthath, au nord; et la frontière tournait à l’orient, vers Thanath-Sélo et passait devant elle, vers l’orient de Janoé.
ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
7 De Janoé, elle descendait à Ataroth et à Naaratha, touchait à Jéricho et aboutissait au Jourdain.
Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
8 De Taphuah, elle allait, du côté de l’occident, au torrent de Cana, pour aboutir à la mer. Tel fut l’héritage des fils d’Ephraïm selon leurs familles.
Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
9 Les fils d’Ephraïm eurent aussi des villes séparées au milieu de l’héritage des fils de Manassé, toutes avec leurs villages.
Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
10 Ils ne chassèrent pas les Chananéens qui habitaient à Gazer, et les Chananéens ont habité jusqu’à ce jour au milieu d’Ephraïm, mais assujettis à la corvée.
Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.