< Josué 14 >

1 Voici ce que les enfants d’Israël reçurent en héritage dans le pays de Chanaan, ce que leur partagèrent le prêtre Eléazar, Josué, fils de Nun, et les chefs de famille des tribus des enfants d’Israël.
Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
2 C’est le sort qui leur assigna leur héritage, comme Yahweh l’avait ordonné par Moïse, pour les neuf tribus et la demi-tribu.
Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
3 Car Moïse avait donné l’héritage des deux tribus et de la demi-tribu de l’autre côté du Jourdain; mais il n’avait pas donné aux Lévites d’héritage parmi eux.
Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
4 Car les fils de Joseph formaient deux tribus, Manassé et Ephraïm; et l’on ne donna pas aux Lévites de part dans le pays, si ce n’est des villes pour habitation et leurs banlieues pour leurs troupeaux et pour leurs biens.
gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
5 Les enfants d’Israël accomplirent l’ordre que Yahweh avait donné à Moïse, et ils partagèrent le pays.
Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 Les fils de Juda s’approchèrent de Josué, à Galgala, et Caleb, fils de Jéphoné, le Cénézéen, lui dit: « Tu sais ce que Yahweh a dit à Moïse, homme de Dieu, à mon sujet et à ton sujet, à Cadès-Barné.
Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
7 J’étais âgé de quarante ans lorsque Moïse, serviteur de Yahweh, m’envoya de Cadès-Barné pour explorer le pays, et je lui fis un rapport dans la sincérité de mon cœur.
Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
8 Tandis que mes frères, qui étaient montés avec moi, découragèrent le peuple, moi, je suivis entièrement Yahweh, mon Dieu.
amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
9 Et ce jour-là Moïse fit ce serment: Le pays que ton pied a foulé sera ton héritage et celui de tes enfants à perpétuité, parce que tu as entièrement suivi Yahweh, mon Dieu.
Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
10 Et maintenant, voici que Yahweh m’a conservé en vie, comme il l’a dit, pendant les quarante-cinq ans écoulés depuis que Yahweh adressa cette parole à Moïse, tandis qu’Israël marchait dans le désert; et maintenant, voici que je suis âgé aujourd’hui de quatre-vingt-cinq ans.
“Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
11 Je suis encore aujourd’hui aussi robuste qu’au jour où Moïse m’envoya; ma force de maintenant est la même que celle d’alors, soit pour combattre, soit pour sortir et pour entrer.
Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
12 Donne-moi donc cette montagne, dont Yahweh a parlé en ce jour-là; car tu as toi-même entendu ce jour-là que là se trouvent des Enacim et des villes grandes et fortifiées; peut-être Yahweh sera-t-il avec moi, et réussirai-je à les chasser, selon qu’a parlé Yahweh. »
Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
13 Josué bénit Caleb, fils de Jéphoné, et il lui donna Hébron en héritage.
Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
14 C’est pourquoi Hébron appartient en héritage à Caleb, fils de Jéphoné, le Cénézéen, jusqu’à ce jour, parce qu’il avait entièrement suivi Yahweh, le Dieu d’Israël.
Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
15 Hébron s’appelait autrefois Cariath-Arbé; Arbé était l’homme le plus grand parmi les Enacim. Et le pays se reposa de la guerre.
(Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.

< Josué 14 >