< Jean 6 >
1 Jésus s’en alla ensuite de l’autre côté de la mer de Galilée ou de Tibériade.
Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya.
2 Et une foule nombreuse le suivait, parce qu’elle voyait les miracles qu’il opérait sur ceux qui étaient malades.
Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya.
3 Jésus monta sur la montagne, et là il s’assit avec ses disciples.
Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.
4 Or la Pâque, la fête des Juifs, était proche.
(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
5 Jésus donc ayant levé les yeux, et voyant qu’une grande foule venait à lui, dit à Philippe: « Où achèterons-nous du pain pour que ces gens aient à manger? »
Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
6 Il disait cela pour l’éprouver, car lui, il savait ce qu’il devait faire.
( Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
7 Philippe lui répondit: « Deux cents deniers de pain ne suffiraient pas pour que chacun en reçoive un morceau. »
Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”
8 Un de ses disciples, André, frère de Simon-Pierre, lui dit:
Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa,
9 « Il y a ici un jeune homme qui a cinq pains d’orge et deux poissons; mais qu’est-ce que cela pour tant de monde? »
“Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?”
10 Jésus dit: « Faites les asseoir. » Il y avait beaucoup d’herbe en ce lieu. Ils s’assirent donc, au nombre d’environ cinq mille.
Yesu ya ce, “ku sa mutane su zauna.”( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Jésus prit les pains, et ayant rendu grâces, il les distribua à ceux qui étaient assis; il leur donna de même des deux poissons, autant qu’ils en voulurent.
Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su.
12 Lorsqu’ils furent rassasiés, il dit à ses disciples: « Recueillez les morceaux qui restent, afin que rien ne se perde. »
Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara.”
13 Ils les recueillirent, et remplirent douze corbeilles des morceaux qui étaient restés des cinq pains d’orge, après qu’ils eurent mangé.
Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci.
14 Ces hommes ayant vu le miracle que Jésus avait fait, disaient: « Celui-ci est vraiment le Prophète qui doit venir dans le monde. »
Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, “Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya.
15 Sachant donc qu’ils allaient venir l’enlever pour le faire roi, Jésus se retira de nouveau, seul, sur la montagne.
“Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
16 Le soir venu, les disciples descendirent au bord de la mer;
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
17 et étant montés dans une barque, ils traversaient la mer dans la direction de Capharnaüm. Il faisait déjà nuit, et Jésus ne les avait pas encore rejoints.
Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.)
18 Cependant la mer, soulevée par un grand vent, était agitée.
Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
19 Quand ils eurent ramé environ vingt-cinq à trente stades, ils virent Jésus marchant sur la mer et s’approchant de la barque; et ils eurent peur.
Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita.
20 Mais il leur dit: « C’est moi, ne craignez point. »
Amma ya ce masu, “Ni ne! kada ku firgita.”
21 Ils voulurent donc le prendre dans la barque, et aussitôt, la barque se trouva au lieu où ils allaient.
Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
22 Le jour suivant, la foule qui était restée de l’autre côté de la mer, avait remarqué qu’il n’y avait là qu’une seule barque, et que Jésus n’y était point entré avec ses disciples, mais que ceux-ci étaient partis seuls.
Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai.
23 — D’autres barques, cependant, étaient arrivées de Tibériade près du lieu où le Seigneur, après avoir rendu grâces, leur avait donné à manger. —
Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
24 La foule donc, ayant vu que Jésus n’était pas là, ni ses disciples non plus, entra dans ces barques et se rendit à Capharnaüm pour chercher Jésus.
Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 Et l’ayant trouvé de l’autre côté de la mer ils lui dirent: « Maître, quand êtes-vous venu ici? »
Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Mallam, yaushe ka zo nan?”
26 Jésus leur repartit et leur dit: « En vérité, en vérité je vous le dis, vous me cherchez, non parce que vous avez vu des miracles, mais parce que vous avez mangé des pains et que vous avez été rassasiés.
Yesu ya amsa masu, da cewa, “hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi.
27 Travaillez, non pour la nourriture qui périt, mais pour celle qui demeure pour la vie éternelle, et que le Fils de l’homme vous donnera. Car c’est lui que le Père, Dieu, a marqué d’un sceau. » (aiōnios )
Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa.” (aiōnios )
28 Ils lui dirent: « Que devons-nous faire, pour faire les œuvres de Dieu? »
Sai suka ce Masa, “Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah?
29 Jésus leur répondit: « Voici l’œuvre que Dieu demande, c’est que vous croyiez en celui qu’il a envoyé. »
Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
30 Ils lui dirent: « Quel miracle faites-vous donc afin que nous le voyions et que nous croyions en vous? Quelles sont vos œuvres?
Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
31 Nos pères ont mangé la manne dans le désert, ainsi qu’il est écrit: Il leur a donné à manger le pain du ciel. »
Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
32 Jésus leur répondit: « En vérité, en vérité, je vous le dis, Moïse ne vous a pas donné le pain du ciel; c’est mon Père qui donne le vrai pain du ciel.
Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
33 Car le pain de Dieu, c’est le pain qui descend du ciel et qui donne la vie au monde. »
Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
34 Ils lui dirent donc: « Seigneur, donnez-nous toujours de ce pain. »
Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
35 Jésus leur répondit: « Je suis le pain de vie: celui qui vient à moi n’aura jamais faim, et celui qui croit en moi n’aura jamais soif.
Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
36 Mais, je vous l’ai dit, vous m’avez vu, et vous ne croyez point.
Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba.
37 Tout ce que le Père me donne viendra à moi, et celui qui vient à moi, je ne le jetterai point dehors;
Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
38 car je suis descendu du ciel pour faire, non ma volonté, mais la volonté de celui qui m’a envoyé.
Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
39 Or la volonté de celui qui m’a envoyé, est que je ne perde aucun de ceux qu’il m’a donnés, mais que je les ressuscite au dernier jour.
Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe.
40 Car c’est la volonté de mon Père [qui m’a envoyé], que quiconque voit le Fils et croit en lui, ait la vie éternelle; et moi je le ressusciterai au dernier jour. » (aiōnios )
Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios )
41 Les Juifs murmuraient à son sujet, parce qu’il avait dit: « Je suis le pain vivant, qui est descendu du ciel. »
Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, “Nine Gurasar da ta sauko daga sama.”
42 Et ils disaient: « N’est-ce pas là Jésus, le fils de Joseph, dont nous connaissons le père et la mère? Comment donc dit-il: Je suis descendu du ciel? »
Suka ce, “Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
43 Jésus leur répondit: « Ne murmurez point entre vous.
Yesu ya amsa, ya ce masu, “Kada ku yi gunaguni a junanku.
44 Nul ne peut venir à moi, si le Père qui m’a envoyé ne l’attire; et moi, je le ressusciterai au dernier jour.
Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe.
45 Il est écrit dans les Prophètes: Ils seront tous enseignés par Dieu. Quiconque a entendu le Père et a reçu son enseignement, vient à moi.
A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
46 Ce n’est pas que personne ait vu le Père, sinon celui qui est de Dieu; celui-là a vu le Père.
Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban.
47 En vérité, en vérité, je vous le dis, celui qui croit en moi a la vie éternelle. (aiōnios )
Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami. (aiōnios )
48 Je suis le pain de vie.
Ni ne Gurasa ta rai.
49 Vos pères ont mangé la manne dans le désert, et ils sont morts.
Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
50 Voici le pain descendu du ciel, afin qu’on en mange et qu’on ne meure point.
Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
51 Je suis le pain vivant qui est descendu du ciel. Si quelqu’un mange de ce pain, il vivra éternellement; et le pain que je donnerai, c’est ma chair, pour le salut du monde. » (aiōn )
Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.” (aiōn )
52 Là-dessus, les Juifs disputaient entre eux, disant: « Comment cet homme peut-il donner sa chair à manger? »
Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, “Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci?
53 Jésus leur dit: « En vérité, en vérité, je vous le dis, si vous ne mangez la chair du Fils de l’homme, et ne buvez son sang, vous n’avez point la vie en vous-mêmes.
Sai Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
54 Celui qui mange ma chair et boit mon sang a la vie éternelle, et moi, je le ressusciterai au dernier jour. (aiōnios )
Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios )
55 Car ma chair est vraiment une nourriture, et mon sang est vraiment un breuvage.
Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 Celui qui mange ma chair et boit mon sang, demeure en moi, et moi en lui.
Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
57 Comme le Père qui est vivant m’a envoyé, et que je vis par le Père, ainsi celui qui me mange vivra aussi par moi.
Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni.
58 C’est là le pain qui est descendu du ciel: il n’en est point comme de vos pères qui ont mangé la manne et sont morts; celui qui mange de ce pain vivra éternellement. » (aiōn )
Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada.” (aiōn )
59 Jésus dit ces choses, enseignant dans la synagogue à Capharnaüm.
Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
60 Beaucoup de ses disciples, l’ayant entendu, dirent: « Cette parole est dure, et qui peut l’écouter? »
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?”
61 Jésus, sachant en lui-même que ses disciples murmuraient à ce sujet, leur dit: « Cela vous scandalise?
Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, “Wannan ya zamar maku laifi?
62 Et quand vous verrez le Fils de l’homme monter où il était auparavant?…
Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da?
63 C’est l’esprit qui vivifie; la chair ne sert de rien. Les paroles que je vous ai dites sont esprit et vie.
Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
64 Mais il y en a parmi vous quelques-uns qui ne croient point. « Car Jésus savait, dès le commencement, qui étaient ceux qui ne croyaient point, et qui était celui qui le trahirait.
Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 Et il ajouta: « C’est pourquoi je vous ai dit que nul ne peut venir à moi, si cela ne lui a été donné par mon Père. »
Ya fada cewa, “shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban.”
66 Dès ce moment, beaucoup de ses disciples se retirèrent, et ils n’allaient plus avec lui.
Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba.
67 Jésus donc dit aux Douze: « Et vous, ne voulez-vous pas aussi vous en aller? »
Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba?
68 Simon-Pierre lui répondit: « Seigneur, à qui irions-nous? Vous avez les paroles de la vie éternelle. (aiōnios )
Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. (aiōnios )
69 Et nous, nous avons cru et nous avons connu que vous êtes le Saint de Dieu. »
Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah.”
70 Jésus leur répondit: « N’est-ce pas moi qui vous ai choisis, vous les Douze? Et l’un de vous est un démon. »
Yesu ya ce masu, “Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?”
71 Il parlait de Judas, fils de Simon Iscariote, car c’était lui qui devait le trahir, lui, l’un des Douze.
Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.