< Jean 12 >

1 Six jours avant la Pâque, Jésus vint à Béthanie, où était Lazare, le mort qu’il avait ressuscité.
Kwana shidda kafin idin ketarewa, Yesu ya zo Baitanya inda Li'azaru yake, wato wannan da Yesu ya tada daga matattu.
2 Là, on lui fit un souper, et Marthe servait. Or, Lazare était de ceux qui se trouvaient à table avec lui.
Sai suka shirya masa abinci a wurin kuma Matta ce ke hidima, Li'azaru kuwa ya kasance cikin wadanda ke kan tebiri tare da Yesu.
3 Marie, ayant pris une livre d’un parfum de nard pur très précieux, en oignit les pieds de Jésus, et les essuya avec ses cheveux; et la maison fut remplie de l’odeur du parfum.
Sai Maryamu ta dauki wani turare da aka yi da man nard, ta shafe kafafun Yesu da shi, ta kuma share kafafun nasa da gashin kanta. Sai gida ya cika da kamshin turaren.
4 Alors un de ses disciples, Judas Iscariote, celui qui devait le trahir, dit:
Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin almajiransa, wanda zai bashe shi, ya ce, “
5 « Pourquoi n’a-t-on pas vendu ce parfum trois cents deniers, pour les donner aux pauvres? »
“Me yasa ba a sayar da wannan turare dinari dari uku a ba gajiyayyu ba?”
6 Il dit cela, non qu’il se souciât des pauvres, mais parce qu’il était voleur, et qu’ayant la bourse, il dérobait ce qu’on y mettait.
Ya fadi haka ba don ya damu da gajiyayyu ba, amma domin shi barawo ne: shi ne ma'aji, kuma yana sata daga jakkar kudi.
7 Jésus lui dit donc: « Laisse-la; elle a gardé ce parfum pour le jour de ma sépulture.
Yesu ya ce, “Ku kyale ta ta ajiye abinda ta tanada domin jana'iza ta.
8 Car vous aurez toujours des pauvres avec vous; mais moi, vous ne m’aurez pas toujours! »
Gajiyayyu suna tare da ku a koyaushe, ni kuwa ba zan kasance da ku koyaushe ba.
9 Un grand nombre de Juifs surent que Jésus était à Béthanie, et ils vinrent, non seulement à cause de Jésus, mais aussi pour voir Lazare qu’il avait ressuscité des morts.
To babban taron Yahudawa sun ji cewa Yesu yana wurin, sai suka zo, ba don Yesu kawai ba amma domin su ga Li'azaru, wanda Yesu ya tada daga matattu.
10 Mais les Princes des prêtres délibérèrent de faire mourir aussi Lazare,
Sai manyan firistoci suka kulla makirci akan yadda za su kashe Li'azaru shima;
11 parce que beaucoup de Juifs se retiraient à cause de lui, et croyaient en Jésus.
domin saboda shi ne yahudawa dayawa suka je suka bada gaskiya ga Yesu.
12 Le lendemain, une multitude de gens qui étaient venus pour la fête, ayant appris que Jésus se rendait à Jérusalem,
Kashegari, babban taro suka zo idin. Da suka ji cewa Yesu na zuwa Urushalima,
13 prirent des rameaux de palmiers, et allèrent au-devant de lui, en criant: « Hosanna! Béni soit celui qui vient au nom du Seigneur, le Roi d’Israël! »
Sai suka dauki ganyen dabino suka fita gari suka tare shi da kira mai karfi suna cewa, “Hosanna! Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila.
14 Jésus, ayant trouvé un ânon, monta dessus, selon ce qui est écrit:
Yesu ya sami wani Aholakin jaki, ya hau kansa; kamar yadda aka rubuta,
15 « Ne crains point, fille de Sion, voici ton Roi qui vient, assis sur le petit d’une ânesse. »
“Kada ki ji tsoro ke 'yar Sihiyona; duba, ga Sarkinki na zuwa, zaune a kan danJaki”.
16 — Ses disciples ne comprirent pas d’abord ces choses; mais lorsque Jésus fut glorifié, ils se souvinrent qu’elles avaient été écrites de lui, et qu’il les avait accomplies en ce qui le regarde. —
Almajiransa basu fahimci wannan al'amari ba da farko, amma bayan da aka daukaka Yesu, sai suka tuna cewa an rubuta wadannan abubuwa game da shi, kuma sun yi masa wadannan abubuwa.
17 La foule donc qui était avec lui lorsqu’il appela Lazare du tombeau et le ressuscita des morts lui rendait témoignage;
Sai taron da ke tare da Yesu a ranar da ya kira Li'azaru daga kabari ya kuma tashe shi daga matattu, suka bada shaida.
18 et c’est aussi parce qu’elle avait appris qu’il avait fait ce miracle, que la multitude s’était portée à sa rencontre.
Domin wannan ne kuma taron suka zo domin su sadu da shi saboda sun ji cewa ya yi wannan alama.
19 Les Pharisiens se dirent donc entre eux: « Vous voyez bien que vous ne gagnez rien; voilà que tout le monde court après lui. »
Don haka, sai farisawa suka shiga magana a tsakanin su suna cewa “Duba, babu abinda zaku iya yi; kun ga, duniya ta gama bin sa.
20 Or, il y avait quelques Gentils parmi ceux qui étaient montés pour adorer, lors de la fête.
Akwai wadansu Helinawa cikin wadanda suka je sujada a idin.
21 Ils s’approchèrent de Philippe, qui était de Bethsaïde en Galilée, et lui firent cette demande: « Seigneur, nous voudrions bien voir Jésus. »
Wadannan suka tafi wurin filibus, mutumin Betsaida da ke Galili, suka ce masa, “Mallam, muna so mu ga Yesu.
22 Philippe alla le dire à André, puis André et Philippe allèrent le dire à Jésus.
Filibus ya tafi ya fadawa Andrawus; sai Andrawus ya tafi tare da Filibus, suka kuwa gaya wa Yesu.
23 Jésus leur répondit: « L’heure est venue où le Fils de l’homme doit être glorifié.
Yesu ya amsa masu ya ce, “sa'a ta zo da za'a daukaka Dan mutum.
24 En vérité, en vérité, je vous le dis, si le grain de blé tombé en terre ne meurt pas, il demeure seul; mais s’il meurt, il porte beaucoup de fruit.
Hakika, hakika, Ina ce maku, in ba kwayar alkama ta fadi kasa ba ta mutu, za ta kasance ita kadai; amma idan ta mutu, za ta bada 'ya'ya masu yawa.
25 Celui qui aime sa vie, la perdra; et celui qui hait sa vie en ce monde, la conservera pour la vie éternelle. (aiōnios g166)
Duk wanda yake son ransa, zai rasa shi; amma wanda ba ya son ransa a duniyan nan za ya kiyaye shi domin rayuwa ta har abada. (aiōnios g166)
26 Si quelqu’un veut être mon serviteur, qu’il me suive, et là où je suis, là aussi sera mon serviteur. Si quelqu’un me sert, mon Père l’honorera.
Idan wani na bauta mani, to bari ya biyo ni; kuma duk inda nike, a can bawana zai kasance kuma. Duk wanda ke bauta mani, Uban zai girmama shi.
27 Maintenant mon âme est troublée; et que dirai-je?… Père, délivrez-moi de cette heure… Mais c’est pour cela que je suis arrivé à cette heure.
Yanzu raina na cikin damuwa, to me zan ce? 'Uba, ka cece ni daga wannan sa'a? Amma Saboda wannan dalili ne na zo wannan sa'a.
28 Père, glorifiez votre nom. » Et une voix vint du ciel: « Je l’ai glorifié et je le glorifierai encore. »
Uba, ka daukaka sunanka”. Sai wata murya daga sama ta ce, “Na daukaka shi, zan kuma sake daukaka shi.
29 La foule qui était là et qui avait entendu, disait: « C’est le tonnerre »; d’autres disaient: « Un ange lui a parlé. »
Daganan sai taron dake tsaye kuma suka ji muryar, suka ce an yi tsawa. Wasu suka ce, “Mala'ika ya yi magana da shi”.
30 Jésus dit: « Ce n’est pas pour moi que cette voix s’est fait entendre, mais pour vous.
Yesu ya amsa ya ce, “wannnan murya ta zo ba saboda ni ba, amma domin ku.”
31 C’est maintenant le jugement de ce monde; c’est maintenant que le Prince de ce monde va être jeté dehors.
Yanzu za'a shar'anta duniya. Yanzu za'a kori mai mulkin duniyan nan.
32 Et moi, quand j’aurai été élevé de la terre, j’attirerai tous les hommes à moi. »
Sa, annan ni, idan an daga ni daga duniya, zan jawo dukan mutane zuwa gare ni”.
33 Ce qu’il disait, pour marquer de quelle mort il devait mourir.
Ya fadi wannan ne domin ya nuna irin mutuwar da za ya yi.
34 La foule lui répondit: « Nous avons appris par la Loi que le Christ demeure éternellement: comment donc dites-vous: il faut que le Fils de l’homme soit élevé? Qui est ce Fils de l’homme? » (aiōn g165)
Taro suka amsa masa cewa, “Mun ji a cikin shari'a cewa Almasihu za ya kasance har abada. Yaya za ka ce, 'za'a daga dan mutum'? Wanene wannan dan mutum?” (aiōn g165)
35 Jésus leur dit: « La lumière n’est plus que pour un temps au milieu de vous. Marchez, pendant que vous avez la lumière, de peur que les ténèbres ne vous surprennent: celui qui marche dans les ténèbres ne sait où il va.
Yesu ya ce masu, “Nan da lokaci kadan za ku kasance da haske, ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya mamaye ku. Wanda ke tafiya cikin duhu, bai san inda za shi ba.
36 Pendant que vous avez la lumière, croyez en la lumière, afin que vous soyez des enfants de lumière. « Jésus dit ces choses, puis s’en allant il se déroba à leurs yeux.
Ku gaskata ga haske tun yana tare da ku domin ku zama yayan haske”. Yesu ya fadi wadannan abubuwa sannan ya tafi ya boye masu.
37 Quoiqu’il eût fait tant de miracles en leur présence, ils ne croyaient point en lui:
Kodashike Yesu ya yi alamu da dama a gabansu, duk da haka ba su gaskata shi ba.
38 afin que fût accompli l’oracle du prophète Isaïe, disant: « Seigneur, qui a cru à notre parole? et à qui le bras du Seigneur a-t-il été révélé? »
Saboda maganar annabi Ishaya ta cika, wadda ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata rahoton mu? Ga wa kuma hannun Ubangiji ya bayyana?
39 Ils ne pouvaient donc croire, parce qu’Isaïe a dit encore:
Saboda wannan dalili basu gaskata ba, gama Ishaya ya sake cewa,
40 « Il a aveuglé leurs yeux et endurci leur cœur, de peur qu’ils ne voient des yeux, qu’ils ne comprennent du cœur, qu’ils ne se convertissent, et que je ne les guérisse. »
ya makantar da su, ya kuma taurare zuciyarsu, saboda kada su gani da idanunsu, su kuma sami fahimta da zuciyarsu, su juyo wurina in warkar da su.
41 Isaïe dit ces choses, lorsqu’il vit la gloire du Seigneur et qu’il parla de lui.
Ishaya ya fadi wadannan abubuwa ne domin ya hangi daukakar Yesu ya kuma yi magana game da shi.
42 Beaucoup, toutefois, même parmi les membres du Sanhédrin, crurent en lui; mais, à cause des Pharisiens, ils ne le confessaient pas, de peur d’être chassés de la synagogue.
Amma duk da haka, dayawa cikin shugabanni suka gaskata Yesu. Amma saboda farisawa, basu shaida shi a sarari ba, domin kada a kore su daga majami'a.
43 Car ils aimèrent la gloire des hommes plus que la gloire de Dieu.
Suna son yabo daga mutane fiye da yabon dake zuwa daga Allah.
44 Or, Jésus éleva la voix et dit: « Celui qui croit en moi, croit, non pas en moi, mais en celui qui m’a envoyé;
Yesu ya yi magana da babbar murya, ya ce, “Wanda ya gaskata ni, ba ni yake gaskatawa kadai ba, amma kuma yana gaskata wanda ya aiko ni,
45 et celui qui me voit, voit celui qui m’a envoyé.
kuma wanda ke gani na, yana ganin shi wanda ya aiko ni.
46 Je suis venu dans le monde comme une lumière, afin que celui qui croit en moi, ne demeure pas dans les ténèbres.
Na zo ne a matsayin haske a duniya, saboda duk wanda ya gaskata da ni ba za ya yi tafiya cikin duhu ba.
47 Si quelqu’un entend ma parole, et ne la garde pas, moi je ne le juge point; car je suis venu, non pour juger le monde, mais pour sauver le monde.
Duk wanda ya ji maganata baya gaskata ba, ba ni hukunta shi; gama ban zo in yi wa duniya hukunci ba, amma don in ceci duniya.
48 Celui qui me méprise et ne reçoit pas ma parole, il a son juge: c’est la parole même que j’ai annoncée; elle le jugera au dernier jour.
Wanda ya ki ni, ya kuma ki ya karbi magana ta, akwai wanda za ya yi masa hukunci. Kalmar da na fada, ita ce za ta yi masa hukunci a rana ta karshe.
49 Car je n’ai point parlé de moi-même; mais le Père, qui m’a envoyé, m’a prescrit lui-même ce que je dois dire et ce que je dois enseigner.
Maganar da ni ke yi, ba ra'ayina ba ne. Amma Uba wanda ya aiko ni shi ke bani umarni game da abin da zan ce da abin da zan fadi.
50 Et je sais que son commandement est la vie éternelle. Les choses donc que je dis, je les dis comme mon Père me les a enseignées. » (aiōnios g166)
Na san umarninsa rai ne madawwami, don haka na ce - kamar yadda Uba ya fada, haka ni ma nake fadi.” (aiōnios g166)

< Jean 12 >