< Job 6 >

1 Alors Job prit la parole et dit:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Oh! S’il était possible de peser mon affliction, et de mettre toutes ensemble mes calamités dans la balance!…
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 Elles seraient plus pesantes que le sable de la mer: voilà pourquoi mes paroles vont jusqu’à la folie.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 Car les flèches du Tout-Puissant me transpercent, et mon âme en boit le venin; les terreurs de Dieu sont rangées en bataille contre moi.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Est-ce que l’onagre rugit auprès de l’herbe tendre? Est-ce que le bœuf mugit devant sa pâture?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Comment se nourrir d’un mets fade et sans sel, ou bien trouver du goût au jus d’une herbe insipide?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 Ce que mon âme se refuse à toucher, c’est là mon pain, tout couvert de souillures.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 Qui me donnera que mon vœu s’accomplisse, et que Dieu réalise mon attente!
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 Que Dieu daigne me briser, qu’il laisse aller sa main et qu’il tranche mes jours!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 Et qu’il me reste du moins cette consolation, que j’en tressaille dans les maux dont il m’accable: de n’avoir jamais transgressé les commandements du Saint!
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 Quelle est ma force, pour que j’attende? Quelle est la durée de mes jours, pour que j’aie patience?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Ma force est-elle la force des pierres, et ma chair est-elle d’airain?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Ne suis-je pas dénué de tout secours, et tout espoir de salut ne m’est-il pas enlevé?
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 Le malheureux a droit à la pitié de son ami, eût-il même abandonné la crainte du Tout-Puissant.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 Mes frères ont été perfides comme le torrent, comme l’eau des torrents qui s’écoulent.
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Les glaçons en troublent le cours, la neige disparaît dans leurs flots.
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 Au temps de la sécheresse, ils s’évanouissent; aux premières chaleurs, leur lit est desséché.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 Dans des sentiers divers leurs eaux se perdent, elles s’évaporent dans les airs, et ils tarissent.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Les caravanes de Théma comptaient sur eux; les voyageurs de Saba espéraient en eux;
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 ils sont frustrés dans leur attente; arrivés sur leurs bords, ils restent confondus.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Ainsi vous me manquez à cette heure; à la vue de l’infortune, vous fuyez épouvantés.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Vous ai-je dit: « Donnez-moi quelque chose, faites-moi part de vos biens,
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 délivrez-moi de la main de l’ennemi, arrachez-moi de la main des brigands? »
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Instruisez-moi, et je vous écouterai en silence; faites-moi voir en quoi j’ai failli.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 Qu’elles ont de force les paroles équitables! Mais sur quoi tombe votre blâme?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Voulez-vous donc censurer des mots? Les discours échappés au désespoir sont la proie du vent.
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 Ah! Vous jetez le filet sur un orphelin, vous creusez un piège à votre ami!
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Maintenant, daignez vous retourner vers moi, et vous verrez si je vous mens en face.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Revenez, ne soyez pas injustes; revenez, et mon innocence apparaîtra.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Y a-t-il de l’iniquité sur ma langue, ou bien mon palais ne sait-il pas discerner le mal?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?

< Job 6 >