< Job 33 >
1 Maintenant donc, Job, écoute mes paroles, prête l’oreille à tous mes discours.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Voilà que j’ouvre la bouche, ma langue forme des mots dans mon palais,
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 mes paroles partiront d’un cœur droit, c’est la vérité pure qu’exprimeront mes lèvres.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 L’esprit de Dieu m’a créé, le souffle du Tout-Puissant me donne la vie.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Si tu le peux, réponds-moi; dispose tes arguments devant moi, tiens-toi ferme.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Devant Dieu je suis ton égal, comme toi j’ai été formé du limon.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Ainsi ma crainte ne t’épouvantera pas, et le poids de ma majesté ne peut t’accabler.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Oui, tu as dit à mes oreilles, et j’ai bien entendu le son de tes paroles;
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 « Je suis pur, exempt de tout péché; je suis irréprochable, il n’y a point d’iniquité en moi.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Et Dieu invente contre moi des motifs de haine, il me traite comme son ennemi.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Il a mis mes pieds dans les ceps, il surveille tous mes pas. »
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Je te répondrai qu’en cela tu n’as pas été juste, car Dieu est plus grand que l’homme.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Pourquoi disputer contre lui, parce qu’il ne rend compte de ses actes à personne?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Pourtant Dieu parle tantôt d’une manière, tantôt d’une autre, et l’on n’y fait pas attention.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Il parle par des songes, par des visions nocturnes, quand un profond sommeil pèse sur les mortels, quand ils dorment sur leur couche.
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 À ce moment, il ouvre l’oreille des hommes, et y scelle ses avertissements,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 afin de détourner l’homme de ses œuvres mauvaises, et d’écarter de lui l’orgueil,
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 afin de sauver son âme de la mort, sa vie des atteintes du dard.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Par la douleur aussi l’homme est repris sur sa couche, quand une lutte continue agite ses os.
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Alors il prend en dégoût le pain, et il a horreur des mets exquis,
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Sa chair s’évanouit aux regards, ses os qu’on ne voyait pas sont mis à nu.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 Il s’approche de la fosse, sa vie est en proie aux horreurs du trépas.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Mais s’il trouve pour intercesseur, un ange entre mille, qui fasse connaître à l’homme son devoir,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 Dieu a pitié de lui et dit à l’ange: « Épargne-lui de descendre dans la fosse, j’ai trouvé la rançon de sa vie. »
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Sa chair alors a plus de fraîcheur qu’au premier âge, il revient aux jours de sa jeunesse.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Il prie Dieu, et Dieu lui est propice; il contemple sa face avec allégresse, et le Très-Haut lui rend son innocence.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Il chante parmi les hommes, il dit: « J’ai péché, j’ai violé la justice, et Dieu ne m’a pas traité selon mes fautes.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Il a épargné à mon âme de descendre dans la fosse, et ma vie s’épanouit à la lumière! »
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Voilà, Dieu fait tout cela, deux fois, trois fois, pour l’homme,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 afin de le ramener de la mort, de l’éclairer de la lumière des vivants.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Sois attentif, Job, écoute-moi; garde le silence, que je parle.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Si tu as quelque chose à dire, réponds-moi; parle, car je voudrais te trouver juste.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Si tu n’as rien à dire, écoute-moi; fais silence, et je t’enseignerai la sagesse.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”