< Job 27 >

1 Job reprit son discours et dit:
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 Par le Dieu vivant qui me refuse justice, par le Tout-Puissant qui remplit mon âme d’amertume:
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 aussi longtemps que j’aurai la respiration, que le souffle de Dieu sera dans mes narines,
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 mes lèvres ne prononceront rien d’inique, ma langue ne proférera pas le mensonge.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Loin de moi la pensée de vous donner raison! Jusqu’à ce que j’expire, je défendrai mon innocence.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 J’ai entrepris ma justification, je ne l’abandonnerai pas; mon cœur ne condamne aucun de mes jours.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 Que mon ennemi soit traité comme le méchant! Que mon adversaire ait le sort de l’impie!
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Quel sera l’espoir de l’impie quand Dieu le retranchera, quand il retirera son âme?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Est-ce que Dieu écoutera ses cris, au jour où l’angoisse viendra sur lui?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Trouve-t-il ses délices dans le Tout-Puissant? Adresse-t-il en tout temps ses prières à Dieu?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Je vous enseignerai la conduite de Dieu, et je ne vous cacherai pas les desseins du Tout-Puissant.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Voici que vous-mêmes, vous avez tous vu; pourquoi donc discourez-vous en vain?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 Voici la part que Dieu réserve au méchant, l’héritage que les violents reçoivent du Tout-Puissant.
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 S’il a des fils en grand nombre, c’est pour le glaive; ses rejetons ne seront pas rassasiés de pain.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Ses survivants seront ensevelis dans la mort, leurs veuves ne les pleureront pas.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 S’il amasse l’argent comme la poussière, s’il entasse les vêtements comme la boue,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 c’est lui qui entasse, mais c’est le juste qui les porte, c’est le juste qui hérite de ton argent.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Sa maison est comme celle que bâtit la teigne, comme la hutte que se construit le gardien des vignes.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Le riche se couche, c’est pour la dernière fois; il ouvre les yeux, il n’est plus.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Les terreurs fondent sur lui comme des eaux, un tourbillon l’enlève au milieu de la nuit.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Le vent d’orient l’emporte, et il disparaît; il l’arrache violemment de sa demeure.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Dieu lance sur lui ses traits sans pitié, il fuit éperdu loin de sa main;
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 on bat des mains à son sujet, de sa demeure on siffle sur lui.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Job 27 >