< Jérémie 9 >
1 Qui changera ma tête en eaux, et mes yeux en source de larmes, pour que je pleure nuit et jour les morts de la fille de mon peuple?
Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
2 Qui me donnera au désert un abri de voyageurs? J’abandonnerai mon peuple, je me retirerai d’avec eux! Car ils sont tous des adultères, une assemblée d’infidèles.
Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
3 Ils bandent leur langue comme leur arc, pour décocher le mensonge; ce n’est pas par la vérité qu’ils sont puissants dans le pays, car ils vont de péché en péché; et ils ne me connaissent pas, — oracle de Yahweh.
“Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
4 Gardez vous chacun de votre ami, et ne vous fiez à aucun frère; car tout frère ne fait que supplanter, et tout ami s’en va répandant la calomnie.
“Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
5 Ils se dupent l’un l’autre; ils ne disent pas la vérité; ils exercent leur langue à mentir; ils s’étudient à mal faire.
Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
6 Tu habites au milieu de la mauvaise foi; c’est par mauvaise foi qu’ils refusent de me connaître, — oracle de Yahweh.
Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
7 C’est pourquoi ainsi parle Yahweh des armées: Je vais les fondre au creuset et les éprouver; car que faire autre chose avec la fille de mon peuple?
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
8 C’est un dard meurtrier que leur langue; elle ne profère que mensonge; de la bouche on dit: Paix à son prochain, et dans le cœur on lui dresse des embûches.
Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
9 Et je ne les punirais pas pour tous ces crimes, — oracle de Yahweh, et d’une nation telle que celle-là je ne me vengerais pas!
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
10 Sur les montagnes je ferai entendre une plainte et une lamentation, sur les pâturages du désert un chant de deuil! Car ils sont brûlés au point que personne n’y passe; on n’y entend plus la voix des troupeaux; depuis l’oiseau du ciel jusqu’au bétail, tous ont fui, ont disparu.
Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
11 Et je ferai de Jérusalem des tas de pierres, un repaire de chacals; et je ferai des villes de Juda une solitude, où personne n’habite.
“Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
12 Quel est l’homme sage qui comprendra ces choses; celui à qui la bouche de Yahweh a parlé, pour qu’il les annonce? Pourquoi le pays est-il détruit, brûlé comme le désert où personne ne passe?
Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
13 Et Yahweh dit: C’est parce qu’ils ont abandonné ma loi, que j’avais mise devant eux, qu’ils n’ont pas écouté ma voix et ne l’ont pas suivie.
Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
14 Mais ils ont marché selon l’obstination de leur cœur, et après les Baals, que leurs pères leur ont enseignés.
A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
15 C’est pourquoi ainsi parle Yahweh, le Dieu d’Israël: « Voici que je vais les nourrir d’absinthe, — ce peuple — et je leur donnerai à boire des eaux empoisonnées.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
16 Je les disperserai parmi des nations que n’ont connues ni eux, ni leurs pères, et j’enverrai contre eux le glaive, jusqu’à ce que je les aie exterminés.
Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
17 Ainsi parle Yahweh des armées: Pensez à commander les pleureuses, et qu’elles viennent! Envoyez vers les plus habiles, et qu’elles viennent!
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
18 Qu’elles se hâtent, qu’elles entonnent sur nous des lamentations; que les larmes coulent de nos yeux, et que de nos paupières les pleurs ruissellent!
Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
19 Car un bruit de lamentations a été entendu dans Sion: « Comment sommes-nous dévastés, couverts de honte, au point d’abandonner le pays, parce qu’on a jeté bas nos demeures? »
An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
20 Femmes, écoutez donc la parole de Yahweh, et que votre oreille reçoive la parole de sa bouche! Enseignez à vos filles une lamentation, et chacune à vos compagnes un chant de deuil.
Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
21 Car la mort est montée par nos fenêtres, et elle est entrée dans nos palais, pour faire disparaître l’enfant de la rue, et les jeunes gens des places publiques.
Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
22 Parle: Ainsi… — oracle de Yahweh: Le cadavre de l’homme tombera, comme du fumier sur un champ, et comme la javelle derrière le moissonneur, sans que personne la ramasse.
Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
23 Ainsi parle Yahweh: Que le sage ne se glorifie pas de sa sagesse; que le fort ne se glorifie pas de sa force; que le riche ne se glorifie pas de sa richesse.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
24 Mais que celui qui se glorifie se glorifie en ceci: d’avoir de l’intelligence et de me connaître. Car je suis Yahweh, qui exerce la miséricorde, le droit et la justice sur la terre; car c’est à cela que je prends plaisir, — oracle de Yahweh.
amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
25 Voici que des jours viennent, — oracle de Yahweh, où je châtierai tout circoncis avec l’incirconcis:
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
26 L’Égypte, Juda, Édom, les fils d’Ammon, Moab, et tous ceux qui se rasent les tempes, qui habitent le désert; car toutes les nations sont incirconcises, et toute la maison d’Israël est incirconcise de cœur.
Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”