< Isaïe 46 >
1 Bel s’écroule, Nébo s’affaisse; on met leurs images sur des animaux, des bêtes de somme; ces idoles que vous portiez sont chargées, comme un fardeau pesant, sur les bêtes fatiguées.
Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
2 Ils s’affaissent, ils s’écroulent ensemble; ils ne peuvent sauver le fardeau; ils s’en vont eux-mêmes en captivité.
Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
3 Écoutez-moi, maison de Jacob, et vous tous, reste de la maison d’Israël, vous dont je me suis chargé dès votre naissance, que j’ai portés dès le sein de votre mère.
“Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
4 Jusqu’à votre vieillesse je serai le même, jusqu’à vos cheveux blancs je vous soutiendrai. Je l’ai déjà fait, et je vous porterai encore; je vous soutiendrai, je vous délivrerai.
Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
5 À qui me comparerez-vous, et de qui me ferez-vous l’égal? À qui m’assimilerez-vous, que nous soyons pareils?
“Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
6 Ils tirent l’or de leur bourse, et pèsent l’argent à la balance; ils engagent un fondeur afin qu’il en fasse un dieu, et ils se prosternent et adorent.
Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
7 Ils le portent sur l’épaule, ils le soutiennent, et vont le poser en son lieu; et il s’y tient sans bouger de sa place. Même lorsqu’on crie vers lui, il ne répond pas, il ne sauve personne de la détresse.
Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
8 Pensez à cela et montrez-vous hommes; rebelles, prenez-le à cœur,
“Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
9 rappelez-vous les choses passées des jours d’autrefois. Oui, moi, je suis Dieu, et il n’y en a point d’autre;
Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
10 je suis Dieu et nul n’est semblable à moi: moi qui, dès le commencement, annonce la fin, et, longtemps à l’avance, ce qui n’est pas encore; qui dis: « Mon dessein subsistera, et je ferai toute ma volonté; »
Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
11 qui de l’Orient appelle l’aigle, d’un pays éloigné l’homme de mon dessein. J’ai parlé, j’accomplirai; j’ai résolu, j’exécuterai!
Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
12 Écoutez-moi, hommes au cœur opiniâtre, qui êtes loin de la justice.
Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
13 Je fais approcher ma justice; elle n’est pas loin, et mon salut ne tardera pas; je donnerai le salut à Sion, ma gloire à Israël.
Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.