< Isaïe 20 >
1 L’année où Thartan vint à Azoth, envoyé par Sargon, roi d’Assyrie, assiégea Azoth et la prit,
A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
2 en ce temps-là, Yahweh parla par le ministère d’Isaïe, fils d’Amos, en disant: « Va, détache le sac qui couvre tes reins, et ôte les sandales de tes pieds. « Et il fit ainsi, marchant nu et déchaussé.
a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
3 Et Yahweh dit: « De même que mon serviteur Isaïe a marché nu et déchaussé; étant pendant trois ans un signe et un présage, pour l’Égypte et pour l’Éthiopie;
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
4 ainsi le roi d’Assyrie emmènera les captifs de l’Égypte, et les déportés de l’Éthiopie, jeunes gens et vieillards, nus et déchaussés, et les reins découverts, à la honte de l’Égypte.
haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
5 Alors ils seront consternés et confus, à cause de l’Éthiopie, qui était leur espoir, et de l’Égypte qui était leur sujet de gloire.
Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
6 Et l’habitant de ce rivage dira en ce jour-là: Voilà ce qu’ est devenu celui en qui nous espérions; celui auprès de qui nous voulions fuir pour chercher du secours, pour être délivrés, des mains du roi d’Assyrie! Et nous, comment échapperons-nous? »
A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”