< Isaïe 14 >

1 Car Yahweh aura pitié de Jacob, et il choisira encore Israël; il les rétablira dans leur pays; les étrangers s'adjoindront à eux, et s'attacheront à la maison de Jacob.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 Les peuples les prendront et les ramèneront chez eux, et la maison d'Israël se les appropriera, sur la terre de Yahweh, comme serviteurs et comme servantes; ils feront captifs ceux qui les avaient faits captifs; et ils domineront sur leurs oppresseurs.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 Et au jour où Yahweh te fera reposer de ton labeur, de tes anxiétés, et de la dure servitude qu'on t'avait imposée,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 tu entonneras cette satire contre le roi de Babylone, et tu diras: Comment a fini le tyran, a cessé l'oppression?
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 Yahweh a brisé le talon des méchants, le sceptre des dominateurs!
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 Il frappait avec fureur les peuples, de coups sans relâche; dans sa colère, il tenait les nations sous le joug par une persécution sans répit.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 Toute la terre est en repos, elle est tranquille, elle éclate en cris d'allégresse.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Les Cyprès mêmes se réjouissent de ta chute, avec les cèdres du Liban: " Depuis que tu es couché là, personne ne monte plus pour nous abattre! "
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Le schéol dans ses profondeurs s'émeut à ton sujet, pour venir à ta rencontre; il réveille pour toi les ombres, tous les monarques de la terre; il fait lever de leurs trônes tous les rois des nations. (Sheol h7585)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
10 Tous, ils prennent la parole pour te dire: " Toi aussi, tu es déchu comme nous, et te voilà semblable à nous! "
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Ton faste est descendu au schéol, avec le son de tes harpes; sous toi sont répandus les vers, et la vermine est ta couverture! (Sheol h7585)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
12 Comment es-tu tombé du ciel, astre brillant, fils de l'aurore? Comment es-tu renversé par terre, toi, le destructeur des nations?
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Toi qui disais en ton cœur: " Je monterai dans les cieux; au-dessus des étoiles de Dieu, j'élèverai mon trône; je m'assiérai sur la montagne de l'assemblée, dans les profondeurs du septentrion;
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 je monterai sur les sommets des nues, je serai semblable au Très-Haut!... "
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Et te voilà descendu au schéol, dans les profondeurs de l'abîme! (Sheol h7585)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
16 Ceux qui te voient fixent sur toi leurs regards, ils te considèrent avec attention: " Est-ce là l'homme qui troublait la terre, qui ébranlait les royaumes,
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 qui faisait du monde un désert, détruisait les villes, et ne laissait pas ses captifs revenir chez eux?
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 Tous les rois des nations, tous, reposent avec honneur, chacun dans sa maison;
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 mais toi, on t'a jeté loin de ton sépulcre, comme un rameau qu'on méprise, couvert de morts, égorgés par l'épée, et précipités dans les flancs rocheux de l'abîme; comme un cadavre qu'on foule aux pieds.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 Tu ne seras pas avec eux dans la tombe car tu as ruiné ton pays, tu as fait périr ton peuple! On ne nommera plus jamais la race des méchants.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Préparez à ses fils un massacre, pour le crime de leurs pères. Qu'ils ne se relèvent pas pour conquérir la terre, qu'ils ne couvrent pas de villes la face du monde!
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 Je me lèverai contre eux, — oracle de Yahweh des armées, — et j'anéantirai de Babylone le nom et le reste, la race et le rejeton, — oracle de Yahweh.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 Et j'en ferai un nid de hérissons, et un étang d'eaux, et je la balaierai avec le balai de la destruction, — oracle de Yahweh des armées.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 Yahweh des armées a juré en disant: " Oui, le dessein qui est arrêté s'accomplira, et ce que j'ai décidé se réalisera.
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 Je briserai Assur dans ma terre, et je le foulerai sur mes montagnes. Alors son joug sera ôté de dessus eux, et son fardeau sera enlevé de leurs épaules.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 C'est là le dessein qui est arrêté contre toute la terre, et c'est là la main qui est étendue contre toutes les nations!
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Car Yahweh des armées a décidé, et qui l'empêcherait? Sa main est étendue, et qui la détournerait? "
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 L'année de la mort du roi Achaz, cet oracle fut prononcé:
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Ne te livre pas à la joie, Philistie tout entière, de ce que la verge qui te frappait a été brisée; car de la race du serpent sortira un basilic, et son fruit sera un dragon volant.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 Alors les plus pauvres trouveront leur pâture, et les malheureux reposeront en sécurité; mais je ferai périr ta race par la faim, et ce qui restera de toi sera exterminé. —
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Hurle, ô porte! Pousse des cris, ô ville! Pâme-toi de frayeur, Philistie tout entière! Car du septentrion vient une fumée, et nul ne se débande dans ses bataillons.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 Que répondra-t-on aux envoyés de la nation? Que Yahweh a fondé Sion, et que les affligés de son peuple y trouvent un refuge.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”

< Isaïe 14 >