< Osée 7 >

1 Quand j’ai voulu guérir Israël, alors s’est révélée l’iniquité d’Éphraïm, et la méchanceté de Samarie; car ils pratiquent le mensonge; le voleur pénètre dans la maison, le brigand se répand au dehors.
a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
2 Et ils ne disent pas en leurs cœurs que je me souviens de toute leur méchanceté. Maintenant leurs forfaits les entourent, ils sont là devant moi.
amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
3 Ils égaient le roi par leur méchanceté, et les princes par leurs mensonges.
“Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
4 Ils sont tous adultères, pareils à un four allumé par le boulanger, qui cesse d’attiser le feu, depuis qu’il a pétri la pâte jusqu’à ce qu’elle soit levée.
Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
5 Au jour de notre roi, les princes se rendent malades par la chaleur du vin; il a étendu sa main avec les moqueurs.
A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
6 Car, dans leur complot, ils ont mis leurs cœurs comme dans un four. Leur boulanger a dormi toute la nuit; le matin, il a été embrasé comme une flamme ardente.
Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
7 Tous sont chauffés comme un four, et ils dévorent leurs juges. Tous leur rois sont tombés, sans qu’aucun d’eux ait crié vers moi.
Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
8 Éphraïm se mêle avec les peuples; Éphraïm est un gâteau qu’on n’a pas retourné.
“Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
9 Des étrangers ont dévoré sa force, et il ne le sait pas; des cheveux blancs parsèment sa tête, et il ne le sait pas.
Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
10 L’orgueil d’Éphraïm témoigne contre lui; ils ne reviennent pas à Yahweh, leur Dieu, et ils ne le recherchent pas, malgré tout cela.
Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
11 Ephraïm est devenu comme une colombe, simple et sans intelligence; ils invoquent l’Égypte, ils vont en Assyrie.
“Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
12 Pendant qu’ils y vont, j’étends sur eux mon filet; je les ferai tomber comme les oiseaux du ciel, je les châtierai comme on l’a annoncé dans leur assemblée.
Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
13 Malheur à eux, car ils ont fui loin de moi! Ruine sur eux, car ils m’ont été infidèles! Et moi, je voudrais les sauver; mais eux disent contre moi des mensonges.
Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
14 Ils ne crient point vers moi dans leur cœur, quand ils se lamentent sur leurs couches. Ils se tourmentent au sujet du froment et du vin nouveau, se détournant de moi.
Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
15 Moi, je les instruisais et je fortifiais leurs bras, et ils méditent le mal contre moi.
Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
16 Ils se tournent, mais non pas en haut; ils sont comme un arc trompeur; leurs chefs tomberont par l’épée à cause de la fureur de leurs langues; et cela fera rire d’eux au pays d’Égypte.
Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.

< Osée 7 >