< Genèse 9 >
1 Dieu bénit Noé et ses fils et leur dit: « Soyez féconds, multipliez et remplissez la terre.
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 Vous serez craints et redoutés de toute bête de la terre, de tout oiseau du ciel, de tout ce qui se meut sur la terre et de tous les poissons de la mer: ils sont livrés entre vos mains.
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Tout ce qui se meut et qui a vie vous servira de nourriture; je vous donne tout cela, comme je vous avais donné l’herbe verte.
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 Seulement vous ne mangerez point de chair avec son âme, c’est-à-dire avec son sang.
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 Et votre sang à vous, j’en demanderai compte à cause de vos âmes, j’en demanderai compte à toute bête; de la main de l’homme, de la main de l’homme qui est son frère, je redemanderai l’âme de l’homme.
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 Quiconque aura versé le sang de l’homme, par l’homme son sang sera versé, car Dieu a fait l’homme à son image.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 Vous, soyez féconds et multipliez; répandez-vous sur la terre et vous y multipliez. »
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 Dieu dit encore à Noé et à ses fils avec lui:
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 « Et moi, je vais établir mon alliance avec vous et avec votre postérité après vous,
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 avec tous les êtres vivants qui sont avec vous, oiseaux, animaux domestiques et toutes les bêtes de la terre avec vous, depuis tous ceux qui sont sortis de l’arche jusqu’à toute bête de la terre.
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 J’établis mon alliance avec vous: aucune chair ne sera plus détruite par les eaux du déluge, et il n’y aura plus de déluge pour ravager la terre. »
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 Et Dieu dit: « Voici le signe de l’alliance que je mets entre moi et vous, et tous les êtres vivants qui sont avec vous, pour toutes les générations à venir.
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 J’ai mis mon arc dans la nue, et il deviendra signe d’alliance entre moi et la terre.
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 Quand j’assemblerai des nuées au-dessus de la terre, l’arc apparaîtra dans la nue,
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 et je me souviendrai de mon alliance entre moi et vous et tout être vivant, de toute chair, et les eaux ne deviendront plus un déluge détruisant toute chair.
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 L’arc sera dans la nue et, en le regardant, je me souviendrai de l’alliance éternelle qui existe entre Dieu et tous les êtres vivants, de toute chair, qui sont sur la terre. »
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 Et Dieu dit à Noé: « Tel est le signe de l’alliance que j’ai établie entre moi et toute chair qui est sur la terre. »
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 Les fils de Noé qui sortirent de l’arche étaient Sem, Cham et Japheth; et Cham était père de Chanaan.
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 Ces trois sont les fils de Noé, et c’est par eux que fut peuplée toute la terre.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 Noé, qui était cultivateur, commença à planter de la vigne.
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 Ayant bu du vin, il s’enivra, et il se découvrit au milieu de sa tente.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 Cham, père de Chanaan, vit la nudité de son père, et il alla le rapporter dehors à ses deux frères.
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 Alors Sem avec Japheth prit le manteau de Noé et, l’ayant mis sur leurs épaules, ils marchèrent à reculons et couvrirent la nudité de leur père.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 Comme leur visage était tourné en arrière, ils ne virent pas la nudité de leur père. Lorsque Noé se réveilla de son ivresse, il apprit ce que lui avait fait son plus jeune fils,
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 et il dit: Maudit soit Chanaan! Il sera pour ses frères le serviteur des serviteurs
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 Puis il dit: Béni soit Yahweh, Dieu de Sem, et que Chanaan soit son serviteur!
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 Que Dieu donne de l’espace à Japheth, qu’il habite dans les tentes de Sem, et que Chanaan soit son serviteur!
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 Noé vécut après le déluge trois cent cinquante ans.
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 Tous les jours de Noé furent de neuf cent cinquante ans, et il mourut.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.