< Genèse 25 >

1 Abraham prit encore une femme, nommée Cétura.
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
2 Et elle lui enfanta Zamran, Jecsan, Madan, Madian, Jesboc et Sué. —
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
3 Jecsan engendra Saba et Dadan; les fils de Dadan furent les Assurim, les Latusim et les Laomim. —
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
4 Les fils de Madian furent Epha, Opher, Hénoch, Abida et Eldaa. — Ce sont là tous les fils de Cétura.
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
5 Abraham donna tous ses biens à Isaac:
Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
6 Quant aux fils de ses concubines, il leur donna des présents, et il les envoya de son vivant loin de son fils Isaac, à l'orient, au pays d'Orient.
Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
7 Voici les jours des années de la vie d'Abraham: il vécut cent soixante-quinze ans.
Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
8 Abraham expira et mourut dans une heureuse vieillesse, âgé et rassasié de jours, et il fut réuni à son peuple.
Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
9 Isaac et Ismaël, ses fils, l'enterrèrent dans la caverne de Macpéla, dans le champ d'Ephron, fils de Séor le Héthéen, qui est vis-à-vis de Mambré:
’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
10 c'est le champ qu'Abraham avait acheté des fils de Heth. Là fut enterré Abraham, avec Sara, sa femme.
filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
11 Après la mort d'Abraham, Dieu bénit Isaac son fils; et Isaac habitait près du puits de Lachaï-Roï.
Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
12 Voici l'histoire d'Ismaël, fils d'Abraham, qu'avait enfanté à Abraham Agar l'Egyptienne, servante de Sara.
Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
13 Voici les noms des fils d'Ismaël, selon les noms de leurs postérités: premier-né d'Ismaël, Nebaïoth; puis Cédar, Adbéel, Mabsam,
Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
14 Masma, Duma, Massa,
Mishma, Duma, Massa,
15 Hadad, Théma, Jéthur, Naphis et Cedma.
Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
16 Ce sont là les fils d'Ismaël, ce sont là leurs noms, selon leurs villages et leurs campements: ce furent les douze chefs de leurs tribus.
Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
17 Voici les années de la vie d'Ismaël: cent trente-sept ans; puis il expira et mourut et il fut réuni à son peuple.
Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
18 Ses fils habitèrent depuis Hévila jusqu'à Sur qui est en face de l'Egypte, dans la direction de l'Assyrie. Il s'étendit en face de tous ses frères.
Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
19 Voici l'histoire d'Isaac, fils d'Abraham. Abraham engendra Isaac.
Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
20 Isaac était âgé de quarante ans quand il prit pour femme Rebecca, fille de Bathuel l'Araméen, de Paddan-Aram, et sœur de Laban, l'Araméen.
Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
21 Isaac implora Yahweh au sujet de sa femme, car elle était stérile; Yahweh l'exauça et Rebecca, sa femme, conçut.
Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
22 Les enfants se heurtaient dans son sein, et elle dit: " S'il en est ainsi, pourquoi suis-je enceinte? " Elle alla consulter Yahweh;
Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
23 et Yahweh lui dit: " Deux nations sont dans ton sein; deux peuples, au sortir de tes entrailles, se sépareront; un peuple l'emportera sur l'autre, et le plus grand servira le plus petit. "
Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
24 Le temps où elle devait enfanter arriva, et voici, il y avait deux jumeaux dans son sein.
Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
25 Celui qui sortit le premier était roux, tout entier comme un manteau de poil, et ils l'appelèrent Esaü; ensuite sortit son frère, tenant dans sa main le talon d'Esaü, et on le nomma Jacob.
Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
26 Isaac était âgé de soixante ans quand ils naquirent.
Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
27 Ces enfants grandirent. Esaü devint un habile chasseur, un homme des champs; mais Jacob était un homme paisible, demeurant sous la tente.
Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
28 Isaac prit en affection Esaü, parce qu'il aimait la venaison, et l'affection de Rebecca était pour Jacob.
Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
29 Comme Jacob faisait un potage, Esaü arriva des champs, accablé de fatigue.
Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
30 Esaü dit à Jacob: " Laisse-moi donc manger de ce roux, de ce roux-là, car je suis fatigué. " — C'est pour cela qu'on a donné à Esaü le nom d'Edom. —
Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
31 Jacob dit: " Vends-moi d'abord ton droit d'aînesse. "
Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
32 Esaü répondit: " Voici je m'en vais mourir; que me servira mon droit d'aînesse? "
Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
33 Et Jacob dit: " Jure-le-moi d'abord. " Il jura et vendit son droit d'aînesse à Jacob.
Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
34 Alors Jacob donna à Esaü du pain et du potage de lentilles; celui-ci mangea et but; puis il se leva et s'en alla. C'est ainsi qu'Esaü méprisa le droit d'aînesse.
Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.

< Genèse 25 >