< 2 Samuel 1 >
1 Après la mort de Saül, David était revenu de battre les Amalécites, et David demeurait depuis deux jours à Siceleg.
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
2 Le troisième jour, voici qu’un homme arriva du camp, d’auprès de Saül, les vêtements déchirés et de la terre sur la tête. Lorsqu’il arriva près de David, il se jeta par terre et se prosterna.
A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
3 David lui dit: « D’où viens-tu? » Et il lui répondit: « Je me suis sauvé du camp d’Israël. »
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
4 David lui dit: « Qu’est-il arrivé? Raconte-le-moi donc. » Il dit: « Le peuple s’est enfui de la bataille, et un grand nombre parmi le peuple sont tombés et ont péri; Saül même et son fils Jonathas sont morts. »
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
5 David dit au jeune homme qui lui apportait ces nouvelles: « Comment sais-tu que Saül et son fils Jonathas sont morts? »
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
6 Et le jeune homme qui lui apportait la nouvelle répondit: « Je me trouvais par hasard sur la montagne de Gelboé; et voici que Saül s’appuyait sur sa lance, et voici que les chars et les cavaliers étaient près de l’atteindre.
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
7 Il se retourna et, m’ayant aperçu, il m’appela, et je dis: « Me voici. »
Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
8 Et il me dit: « Qui es-tu? » Je lui répondis: « Je suis un Amalécite. »
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
9 Et il me dit: « Approche-toi donc de moi et donne-moi la mort; car je suis pris de vertige, et ma vie est encore tout entière en moi.
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 Je m’approchai de lui et je lui donnai la mort, car je savais bien qu’il ne survivrait pas à sa défaite. J’ai pris le diadème qui était sur sa tête et le bracelet qu’il avait au bras, et je les apporte ici à mon seigneur. »
“Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 David saisit ses vêtements et les déchira, et tous les hommes qui étaient auprès de lui firent de même.
Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
12 Ils célébrèrent leur deuil, pleurant et jeûnant jusqu’au soir, sur Saül, sur son fils Jonathas, sur le peuple de Yahweh et sur la maison d’Israël, parce qu’ils étaient tombés par l’épée.
Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 David dit au jeune homme qui lui avait apporté la nouvelle: « D’où es-tu? » Il répondit: « Je suis fils d’un étranger, d’un Amalécite. »
Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 David lui dit: « Comment n’as-tu pas craint d’étendre ta main pour donner la mort à l’oint de Yahweh? »
Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 Et David, appelant un des jeunes gens, dit: « Approche et tue-le. » Cet homme frappa l’ Amalécite, et il mourut.
Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
16 Et David lui dit: « Que ton sang soit sur ta tête! Car ta bouche a déposé contre toi quand tu as dit: C’est moi qui ai donné la mort à l’oint de Yahweh. »
Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
17 David entonna ce chant funèbre sur Saül et sur Jonathas, son fils,
Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
18 et il ordonna de l’enseigner aux enfants de Juda; c’est le chant de l’Arc. Voici qu’il est écrit dans le Livre du Juste:
Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 La splendeur d’Israël a-t-elle péri sur tes hauteurs? Comment sont tombés les héros?
“Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
20 Ne l’annoncez pas à Geth, ne le publiez pas dans les rues d’Ascalon, de peur que les filles des Philistins ne s’en réjouissent, de peur que les filles des incirconcis ne sautent de joie!
“Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
21 Montagnes de Gelboé, qu’il n’y ait sur vous ni rosée ni pluie, ni champs de prémices! Car là fut jeté bas le bouclier des héros. Le bouclier de Saül n’était pas oint d’huile,
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
22 mais du sang des blessés, de la graisse des vaillants; l’arc de Jonathas ne recula jamais en arrière, et l’épée de Saül ne revenait pas inactive.
“Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Saül et Jonathas, chéris et aimables dans la vie et dans la mort, ils ne furent point séparés. Ils étaient plus agiles que les aigles, ils étaient plus forts que les lions.
Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
24 Filles d’Israël, pleurez sur Saül, qui vous revêtait de pourpre au sein des délices, qui mettait des ornements d’or sur vos vêtements!
“Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
25 Comment les héros sont-ils tombés dans la bataille? Jonathas a été percé sur tes hauteurs!
“Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 L’angoisse m’accable à cause de toi, Jonathas, mon frère. Tu faisais toutes mes délices; ton amour m’était plus précieux que l’amour des femmes.
Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
27 Comment les héros sont-ils tombés? Comment les guerriers ont-ils péri?
“Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”