< 2 Rois 3 >

1 Joram, fils d’Achab, devint roi d’Israël à Samarie la dix-huitième année de Josaphat, roi de Juda; et il régna douze ans.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Il fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh, non pas toutefois comme son père et sa mère; car il fit disparaître la stèle de Baal, que son père avait faite.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Mais il s’attacha aux péchés de Jéroboam, fils de Nabat, qui avait fait pécher Israël, et il ne s’en détourna point.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Mésa, roi de Moab, possédait des troupeaux, et il payait au roi d’Israël un tribut de cent mille agneaux et de cent mille béliers avec leurs toisons.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 À la mort d’Achab, le roi de Moab se révolta contre le roi d’Israël.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Le roi Joram sortit donc en ce jour-là de Samarie et passa en revue tout Israël.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 S’étant mis en marche, il envoya dire à Josaphat, roi de Juda: « Le roi de Moab s’est révolté contre moi; viendras-tu avec moi attaquer Moab? » Josaphat répondit: « Je monterai; il en sera de moi comme de toi, de mon peuple comme de ton peuple, de mes chevaux comme de tes chevaux. »
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Et il dit: « Par quel chemin monterons-nous? » Joram répondit: « Par le chemin du désert d’Edom. »
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Le roi d’Israël, le roi de Juda et le roi d’Edom partirent. Après une marche de sept jours, il n’y eut point d’eau pour l’armée et pour les bêtes qui la suivaient.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Alors le roi d’Israël dit: « Hélas! Yahweh a appelé ces trois rois pour les livrer aux mains de Moab! »
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Mais Josaphat dit: « N’y a-t-il ici aucun prophète de Yahweh, par qui nous puissions consulter Yahweh? » Un des serviteurs du roi d’Israël répondit et dit: « Il y a ici Élisée, fils de Saphat, qui versait l’eau sur les mains d’Élie. »
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 Et Josaphat dit: « La parole de Yahweh est avec lui. » Le roi d’Israël, Josaphat, roi de Juda, et le roi d’Edom descendirent auprès de lui.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Élisée dit au roi d’Israël: « Que me veux-tu, toi? Va vers les prophètes de ton père et vers les prophètes de ta mère. » Et le roi d’Israël lui dit: « Non, car Yahweh a appelé ces trois rois pour les livrer entre les mains de Moab. »
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Élisée dit: « Yahweh des armées, devant qui je me tiens, est vivant! Si je n’avais égard à Josaphat, roi de Juda, je ne ferais aucune attention à toi et je ne te regarderais pas.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Maintenant, amenez-moi un joueur de harpe. » Et pendant que le joueur de harpe jouait, la main de Yahweh fut sur Élisée;
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 et il dit: « Ainsi dit Yahweh: Faites dans cette vallée des fosses et des fosses.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Car ainsi dit Yahweh: Vous ne verrez point de vent et vous ne verrez point de pluie, et cette vallée se remplira d’eau, et vous boirez, vous, vos troupeaux et vos bêtes de somme.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Mais cela est peu de chose aux yeux de Yahweh: il livrera Moab entre vos mains.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 Vous frapperez toutes les villes fortes et toutes les villes de choix, vous abattrez tous les arbres fruitiers, vous boucherez toutes les sources d’eau, et vous désolerez, en les couvrant de pierres, tous les meilleurs champs. »
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 De fait le matin, à l’heure où l’on offre l’oblation, voici que l’eau arriva par le chemin d’Edom, et le pays fut rempli d’eau.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Cependant, tous les Moabites ayant appris que les rois montaient pour les attaquer, on convoqua tous les hommes capables de ceindre le baudrier, et même au-delà, et ils se postèrent sur la frontière.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Ils se levèrent de bon matin et, quand le soleil brilla sur les eaux, les Moabites virent en face d’eux les eaux rouges comme du sang.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 Ils dirent: « C’est du sang! Les rois sont détruits, ils se sont frappés les uns les autres; et maintenant Moabites, au pillage! »
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Et ils s’avancèrent vers le camp d’Israël. Mais les Israélites se levèrent et frappèrent Moab, qui prit la fuite devant eux. Pénétrant dans le pays, ils frappèrent Moab;
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 ils détruisirent les villes; chacun jetant sa pierre dans tous les meilleurs champs, ils les en remplirent; ils bouchèrent toutes les sources d’eau, ils abattirent tous les arbres fruitiers, au point que de Qir-Charoseth il ne resta que les pierres; les frondeurs l’avaient entourée et battue.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Quand le roi de Moab vit qu’il avait le dessous dans le combat, il prit avec lui sept cents hommes, l’épée nue à la main, pour se frayer un passage jusqu’au roi d’Edom; mais ils ne purent y réussir.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Prenant alors son fils premier-né, qui devait régner à sa place, il l’offrit en holocauste sur la muraille. Et une grande indignation s’empara d’Israël; et ils s’éloignèrent du roi de Moab et retournèrent dans leur pays.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< 2 Rois 3 >