< 2 Rois 21 >
1 Manassé avait douze ans lorsqu’il devint roi, et il régna cinquante-cinq ans à Jérusalem. Sa mère s’appelait Haphsiba.
Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
2 Il fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh, imitant les abominations des nations que Yahweh avait chassées devant les enfants d’Israël.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Il rebâtit les hauts lieux qu’Ézéchias, son père avait détruits; il éleva des autels à Baal, il fit une aschérah, comme avait fait Achab, roi d’Israël, et il se prosterna devant toute l’armée du ciel et la servit.
Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
4 Il bâtit des autels dans la maison de Yahweh, de laquelle Yahweh avait dit: « C’est dans Jérusalem que je placerai mon nom. »
Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
5 Il bâtit des autels à toute l’armée du ciel dans les deux parvis de la maison de Yahweh.
Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
6 Il fit passer son fils par le feu; il pratiquait les augures et la divination; il institua des nécromanciens et des sorciers: faisant ainsi de plus en plus ce qui est mal aux yeux de Yahweh, de manière à l’irriter.
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
7 Il mit l’idole d’Astarté, qu’il avait faite, dans la maison dont Yahweh avait dit à David et à Salomon, son fils: « C’est dans cette maison et c’est dans Jérusalem, que j’ai choisie parmi toutes les tribus d’Israël, que je veux placer mon nom pour toujours.
Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Je ne ferai plus errer le pied d’Israël hors du pays que j’ai donné à ses pères, pourvu seulement qu’ils aient soin de mettre en pratique tout ce que je leur ai commandé et toute la loi que leur a prescrite mon serviteur Moïse. »
Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
9 Mais ils n’obéirent point; et Manassé les égara, au point qu’ils firent le mal plus que toutes les nations que Yahweh avait détruites devant les enfants d’Israël.
Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 Alors Yahweh parla par l’organe de ses serviteurs les prophètes, en ces termes:
Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
11 « Parce que Manassé, roi de Juda, a commis ces abominations, parce qu’ il a fait pire que tout ce qu’avaient fait avant lui les Amorrhéens, et parce qu’ il a fait aussi pécher Juda par ses idoles,
“Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
12 voici ce que dit Yahweh, Dieu d’Israël: Voici que je vais faire venir sur Jérusalem et sur Juda des malheurs tels que les deux oreilles tinteront à qui en entendra parler.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
13 J’étendrai sur Jérusalem le cordeau de Samarie et le niveau de la maison d’Achab, et je nettoierai Jérusalem comme le plat qu’on nettoie et qu’on retourne sur sa face après l’avoir nettoyé.
Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
14 J’abandonnerai le reste de mon héritage, et je les livrerai entre les mains de leurs ennemis, et ils deviendront la proie et le butin de tous leurs ennemis:
Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
15 parce qu’ils ont fait ce qui est mal à mes yeux, et qu’ils m’ont irrité depuis le jour où leurs pères sont sortis d’Égypte jusqu’à présent. »
domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
16 Manassé répandit aussi beaucoup de sang innocent, jusqu’à en remplir Jérusalem d’un bout à l’autre, outre ses péchés par lesquels il fit pécher Juda, l’entraînant à faire ce qui est mal aux yeux de Yahweh.
Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
17 Le reste des actes de Manassé, tout ce qu’il a fait, et les péchés qu’il a commis, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
18 Manassé se coucha avec ses pères, et il fut enterré dans le jardin de sa maison, dans le jardin d’Oza. Amon, son fils, régna à sa place.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
19 Amon avait vingt-deux ans lorsqu’il devint roi, et il régna deux ans à Jérusalem. Sa mère s’appelait Messalemeth, fille de Harus, de Jétéba.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
20 Il fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh, comme avait fait Manassé, son père;
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
21 il marcha dans toute la voie où avait marché son père, il servit les idoles que son père avait servies, et il se prosterna devant elles;
Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
22 il abandonna Yahweh, le Dieu de ses pères, et il ne marcha pas dans la voie de Yahweh.
Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
23 Les serviteurs d’Amon conspirèrent contre lui et tuèrent le roi dans sa maison.
Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
24 Mais le peuple du pays frappa tous ceux qui avaient conspiré contre le roi Amon; et le peuple du pays établit roi Josias, son fils, à sa place.
Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
25 Le reste des actes d’Amon, et ce qu’il a fait, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.