< 2 Chroniques 15 >

1 L'Esprit de Dieu vint sur Azarias, fils d'Oded,
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Azariya ɗan Oded.
2 qui alla au-devant d'Asa et lui dit: " Ecoutez-moi, Asa, et tout Juda et tout Benjamin. Yahweh est avec vous quand vous êtes avec lui; si vous le cherchez, il se laissera trouver par vous; mais si vous l'abandonnez, il vous abandonnera.
Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.
3 Pendant longtemps Israël a été sans vrai Dieu, sans prêtre qui enseignât, sans loi;
Tun da daɗewa Isra’ila ba su da Allah na gaskiya, babu firist da zai koyar, kuma babu doka.
4 mais, dans sa détresse, il s'est retourné vers Yahweh, son Dieu; ils l'ont cherché, et s'est laissé trouver par eux.
Amma cikin wahalarsu suka juya ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka kuma neme shi, suka kuwa same shi.
5 Dans ces temps-là, point de sécurité pour ceux qui allaient et venaient, car de grandes confusions pesaient sur tous les habitants des pays.
A waɗancan kwanaki akwai hatsari a yin tafiye-tafiye, gama dukan mazaunan ƙasashe suna cikin babbar damuwa.
6 On se heurtait, peuple contre peuple, ville contre ville, parce que Dieu les agitait par toutes sortes de tribulations.
Wata ƙasa takan murƙushe wata, wani birni kuma yakan murƙushe wani, domin Allah ya wahalshe su da kowace irin damuwa.
7 Vous donc, montrez-vous forts, et que vos mains ne faiblissent pas, car il y aura récompense pour vos œuvres. "
Amma game da ku, ku ƙarfafa kada ku fid da zuciya, gama za a ba ku ladan aikinku.”
8 En entendant ces paroles, la prophétie d'Oded, le prophète, Asa prit courage; il fit disparaître les abominations de tout le pays de Juda et de Benjamin et des villes qu'il avait prises dans la montagne d'Ephraïm, et restaura l'autel de Yahweh qui était devant le portique de Yahweh.
Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
9 Il rassembla tout Juda et Benjamin, et ceux d'Ephraïm, de Manassé et de Siméon qui étaient venus séjourner parmi eux; car un grand nombre de gens d'Israël avaient passé de son côté, en voyant que Yahweh, son Dieu, était avec lui.
Sa’an nan ya tattara dukan Yahuda da Benyamin da kuma mutane daga Efraim, Manasse da Simeyon waɗanda suke zaune a cikinsu, gama jama’a mai girma ta zo wurinsa daga Isra’ila sa’ad da suka ga cewa Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
10 Ils s'assemblèrent à Jérusalem le troisième mois de la quinzième année du règne d'Asa.
Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta mulkin Asa.
11 Ce jour-là, ils immolèrent à Yahweh, sur le butin qu'ils avaient amené, sept cents bœufs et sept mille brebis.
A lokacin suka miƙa hadaya bijimai ɗari bakwai da tumaki da kuma awaki dubu bakwai ga Ubangiji daga ganimar da suka dawo da ita.
12 Ils prirent l'engagement solennel de chercher Yahweh, le Dieu de leurs pères, de tout leur cœur et de toute leur âme,
Suka yi alkawari don su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, da dukan zuciyarsu da kuma dukan ransu.
13 et quiconque ne rechercherait pas Yahweh, le Dieu d'Israël, serait mis à mort, le petit comme le grand, l'homme comme la femme.
Aka kashe dukan waɗanda ba su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, ko ƙarami ko babba, namiji ko ta mace.
14 Ils firent un serment à Yahweh à haute voix, avec des cris d'allégresse, au son des trompettes et des cors;
Suka yi rantsuwa ga Ubangiji da babbar murya, da ihu da garayu da ƙahoni.
15 tout Juda fut dans la joie de ce serment, car ils avaient juré de tout leur cœur; car c'est de leur pleine volonté qu'ils avaient cherché Yahweh, et il s'était laissé trouver par eux; et Yahweh leur donna la paix tout à l'entour.
Dukan Yahuda suka yi farin ciki game da rantsuwar domin sun yi rantsuwar gabagadi. Suka nemi Allah da gaske, suka kuma same shi. Saboda haka Ubangiji ya ba su hutu a kowane gefe.
16 Le roi Asa ôta même à Maacha, sa mère, la dignité de reine-mère, parce qu'elle avait fait une idole abominable pour Astarté. Asa abattit son idole abominable et, l'ayant réduite en poudre, il la brûla au torrent de Cédron.
Sarki Asa ya tuɓe mahaifiyar mahaifiyarsa daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, domin ta gina ginshiƙin banƙyama na Ashera. Asa ya rurrushe shi, ya farfasa shi ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
17 Mais les hauts lieux ne disparurent point d'Israël, quoique le cœur d'Asa fut parfait pendant toute sa vie.
Ko da yake bai kawar da masujadan kan tudu daga Isra’ila ba, zuciyar Asa ta cika da bin Ubangiji dukan kwanakinsa.
18 Il déposa dans la maison de Dieu les choses consacrées par son père et les choses consacrées par lui-même, de l'argent, de l'or et des vases.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyaki a haikalin Allah waɗanda shi da mahaifinsa suka keɓe.
19 Il n'y eut point de guerre jusqu'à la trente-cinquième année du règne d'Asa.
Ba a ƙara yin yaƙi ba sai a shekara ta talatin da biyar ta mulkin Asa.

< 2 Chroniques 15 >