< 1 Samuel 9 >

1 Il y avait un homme de Benjamin, nommé Cis, fils d’Abiel, fils de Séror, fils de Bécorath, fils d’Aphia, fils d’un Benjamite; c’était un homme vaillant.
An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
2 Il avait un fils du nom de Saül, jeune et beau; aucun des enfants d’Israël n’était plus beau que lui, et il dépassait de la tête tout le peuple.
Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
3 Les ânesses de Cis, père de Saül, s’étaient égarées, et Cis dit à Saül, son fils: « Prends avec toi un des serviteurs, lève-toi et va à la recherche des ânesses. »
To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
4 Il traversa la montagne d’Ephraïm et traversa le pays de Salisa, et ils ne les trouvèrent pas; ils traversèrent le pays de Salisa, et elles n’y étaient pas; il traversa le pays de Benjamin, et ils ne les trouvèrent pas.
Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
5 Lorsqu’ils furent arrivés au pays de Suph, Saül dit à son serviteur qui l’accompagnait: « Viens, retournons, de peur que mon père, oubliant les ânesses, ne soit en peine à notre sujet. »
Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
6 Le serviteur lui dit: « Voici qu’il y a dans cette ville un homme de Dieu; c’est un homme très considéré, tout ce qu’il dit arrive sûrement. Allons-y donc; peut-être nous fera-t-il connaître le chemin que nous devons prendre. »
Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
7 Saül dit à son serviteur: « Si nous y allons, qu’apporterons-nous à l’homme de Dieu? Car il n’y a plus de vivres dans nos sacs, et nous n’avons aucun présent à offrir à l’homme de Dieu. Qu’avons-nous? »
Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
8 Le serviteur répondit encore et dit à Saül: « Voici que je trouve sur moi le quart d’un sicle d’argent; je le donnerai à l’homme de Dieu, et il nous indiquera notre chemin. »
Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
9 — Autrefois, en Israël, on disait, en allant consulter Dieu: « Venez et allons au voyant. » Car celui qu’on appelle aujourd’hui prophète s’appelait autrefois voyant. —
(A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
10 Saül dit à son serviteur: « Ton avis est bon; viens, allons. » Et ils se rendirent à la ville où était l’homme de Dieu.
Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
11 Comme ils gravissaient la montée qui mène à la ville, ils rencontrèrent des jeunes filles sorties pour puiser de l’eau, et ils leur dirent: « Le voyant est-il ici? »
Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
12 Elles leur répondirent en disant: « Oui, il y est, le voilà devant toi; mais va promptement, car il est venu aujourd’hui à la ville, parce que le peuple a aujourd’hui un sacrifice sur le haut lieu.
’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
13 Dès votre entrée dans la ville, vous le trouverez, avant qu’il monte au haut lieu pour le repas; car le peuple ne mangera point qu’il ne soit arrivé, parce qu’il doit bénir le sacrifice; après quoi, les conviés mangeront. Montez donc maintenant, vous le trouverez aujourd’hui. »
Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
14 Et ils montèrent à la ville. Ils étaient entrés au milieu de la ville, et voici que Samuel sortait à leur rencontre, pour monter en haut lieu.
Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
15 Or, un jour avant l’arrivée de Saül, Yahweh avait fait une révélation à Samuel, en disant:
Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
16 « Demain, à cette heure, je t’enverrai un homme du pays de Benjamin, et tu l’oindras pour être le chef de mon peuple d’Israël, et il délivrera mon peuple de la main des Philistins; car j’ai regardé mon peuple, parce que son cri est venu jusqu’à moi. »
“Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
17 Dès que Samuel eut vu Saül, Yahweh lui dit: « Voici l’homme dont je t’ai parlé; c’est lui qui régnera sur mon peuple. »
Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
18 Saül s’approcha de Samuel au milieu de la porte, et dit: « Indique-moi, je te prie, où est la maison du voyant. »
Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
19 Samuel répondit à Saül: « C’est moi qui suis le voyant. Monte devant moi au haut lieu, et vous mangerez aujourd’hui avec moi; je te laisserai partir demain, et je te dirai tout ce qu’il y a dans ton cœur.
Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
20 Quant aux ânesses que tu as perdues il y a trois jours, ne t’en inquiète pas, car elles sont retrouvées. Et à qui sera tout ce qu’il y a de précieux en Israël? N’est-ce pas à toi et à toute la maison de ton père? »
Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
21 Saül répondit: « Ne suis-je pas Benjamite, de la plus petite des tribus d’Israël? et ma famille n’est-elle pas la moindre de toutes les familles de la tribu de Benjamin? Pourquoi m’as-tu dit une telle parole? »
Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
22 Samuel, ayant pris Saül et son serviteur, les fit entrer dans la salle et leur donna la première place parmi les conviés, qui étaient environ trente hommes.
Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
23 Samuel dit au cuisinier: « Sers la portion que je t’ai remise et dont je t’ai dit: mets-la à part. »
Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
24 Le cuisinier leva l’épaule avec ce qui l’entoure, et il la servit à Saül. Et Samuel dit: « Voici la portion réservée; prends-la devant toi et mange, car elle a été gardée pour ce moment lorsque j’ai convoqué le peuple. » Et Saül mangea avec Samuel ce jour-là.
Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
25 Ils descendirent ensuite du haut lieu dans la ville, et Samuel s’entretint avec Saül sur le toit.
Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
26 Le lendemain, ils se levèrent de bon matin et, comme l’aurore montait, Samuel appela Saül sur le toit, et dit: « Lève-toi, et je te laisserai aller. » Saül se leva, et ils sortirent tous deux, lui et Samuel.
Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
27 Quand ils furent descendus à l’extrémité de la ville, Samuel dit à Saül: « Dis à ton serviteur de passer devant nous; » et le serviteur prit les devants. « Arrête-toi maintenant, ajouta Samuel, et je te ferai entendre ce que Dieu a dit. »
Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”

< 1 Samuel 9 >