< 1 Samuel 20 >

1 David s’enfuit de Naioth en Rama et, étant venu, il dit devant Jonathas: « Qu’ai-je fait? quel est mon crime, quel est mon péché devant ton père, pour qu’il en veuille à ma vie? »
Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
2 Jonathas lui dit: « Loin de là! Tu ne mourras point. Mon père ne fait aucune chose, grande ou petite, sans m’en faire part; pourquoi donc me cacherait-il celle-là? Il n’en est rien. »
Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
3 David répondit avec un serment: « Ton père sait bien que j’ai trouvé grâce à tes yeux, et il aura dit: Que Jonathas ne le sache pas, de peur qu’il en ait de la peine. Mais, aussi vrai que Yahweh est vivant et que ton âme est vivante! il n’y a qu’un pas entre la mort et moi. »
Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
4 Jonathas dit à David: « Tout ce que ton âme dira, je le ferai pour toi. »
Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
5 Et David dit à Jonathas: « Voici, c’est demain la nouvelle lune, et je devrais m’asseoir auprès du roi pour le repas; laisse-moi partir, et je me cacherai dans les champs jusqu’au soir du troisième jour.
Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
6 Si ton père s’aperçoit de mon absence, tu lui diras: David m’a prié de lui laisser faire une course à Bethléem, sa ville, parce qu’il y a là le sacrifice annuel pour toute sa famille.
In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
7 S’il dit: C’est bien! ton serviteur peut être en paix; mais s’il se met en colère, sache que le mal est bien résolu de sa part.
In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
8 Use donc de bonté envers ton serviteur, puisque c’est par une alliance au nom de Yahweh que tu as attiré vers toi ton serviteur. S’il y a quelque faute en moi, mets-moi à mort toi-même, car pourquoi me mènerais-tu à ton père? »
Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
9 Jonathas lui dit: « Loin de toi cette pensée! Car si j’apprends vraiment que le mal est résolu de la part de mon père pour venir sur toi, je jure de t’en informer. »
Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
10 David dit à Jonathas: « Qui m’informera de cela ou de ce que ton père répondrait de fâcheux? »
Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
11 Jonathas dit à David: « Viens, sortons dans les champs »; et ils sortirent tous deux dans les champs.
Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
12 Jonathas dit à David: « Yahweh, Dieu d’Israël! Je sonderai mon père demain ou après-demain, et si cela va bien pour David, et que je n’envoie pas vers toi pour t’en informer,
Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
13 que Yahweh traite Jonathas dans toute sa rigueur! S’il plaît à mon père de te faire du mal, je t’en informerai aussi et je te ferai partir, afin que tu t’en ailles en paix, et que Yahweh soit avec toi, comme il a été avec mon père!
Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
14 Et si je suis encore vivant, veuille user envers moi de la bonté de Yahweh, et, si je meurs,
Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
15 ne pas retirer à jamais ta bonté de ma maison, pas même lorsque Yahweh retranchera de dessus la face de la terre chacun des ennemis de David! »
Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
16 C’est ainsi que Jonathas fit alliance avec la maison de David, et que Yahweh tira vengeance des ennemis de David.
Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
17 Jonathas adjura encore une fois David par l’amour qu’il avait pour lui, car il l’aimait comme son âme.
Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
18 Jonathas lui dit: « C’est demain la nouvelle lune; on remarquera que ta place est vide.
Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
19 Le troisième jour, tu descendras promptement et tu viendras au lieu où tu étais caché, au jour de l’affaire, et tu resteras près de la pierre d’Ezel.
Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
20 Je tirerai trois flèches du côté de la pierre, comme si je visais à un but.
Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
21 Et voici, j’enverrai le garçon en lui disant: Va, retrouve les flèches. Si je dis au garçon: Voici, les flèches sont en deçà toi, prends-les! alors, viens, car tout va bien pour toi, et il n’y a nul danger, Yahweh est vivant!
Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
22 Mais si je parle ainsi au garçon: Voici, les flèches sont au delà de toi, alors va-t-en, car Yahweh te fait partir.
Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
23 Et quant à la parole que nous avons dite, moi et toi, voici que Yahweh est à jamais entre toi et moi. »
Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
24 David se cacha dans les champs. La nouvelle lune venue, le roi prit place au festin pour manger;
Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
25 comme à l’ordinaire, le roi s’assit sur son siège, sur le siège qui était près du mur; Jonathas se leva, et Abner s’assit à côté de Saül et la place de David resta vide.
Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
26 Saül ne dit rien ce jour-là, car, disait-il, « quelque chose lui est arrivé; il n’est pas pur, certainement il n’est pas pur. »
Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
27 Le lendemain, second jour de la nouvelle lune, la place de David était encore vide; et Saül dit à Jonathas, son fils: « Pourquoi le fils d’Isaï n’est-il pas venu au repas, ni hier ni aujourd’hui? »
Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
28 Jonathas répondit à Saül: « David m’a demandé avec instances la permission d’aller jusqu’à Bethléem.
Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
29 Il a dit: Laisse-moi aller, je te prie, car nous avons dans la ville un sacrifice de famille, et mon frère m’a commandé d’y assister; si donc j’ai trouvé grâce à tes yeux, permets que je m’y rende et que je voie mes frères! C’est pourquoi il n’est pas venu à la table du roi. »
Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
30 Alors la colère de Saül s’enflamma contre Jonathas, et il lui dit: « Fils d’une femme perverse et rebelle, ne sais-je pas que tu as pour ami le fils d’Isaï, à ta honte et à la honte de la nudité de ta mère?
Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
31 Car aussi longtemps que le fils d’Isaï sera vivant sur la terre, il n’y aura de sécurité ni pour toi, ni pour ta royauté. Et maintenant, envoie-le prendre et amène-le -moi, car c’est un fils de la mort. »
Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
32 Jonathas répondit à Saül, son père, et lui dit: « Pourquoi serait-il mis à mort? Qu’a-t-il fait? »
Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
33 Et Saül brandit sa lance contre lui pour le frapper. Jonathas comprit que c’était chose arrêtée chez son père de faire périr David.
Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
34 Jonathas se leva donc de table dans une violente colère, et ne prit point de nourriture, le second jour de la nouvelle lune; car il était affligé à cause de David, parce que son père l’avait outragé.
Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
35 Le lendemain matin, Jonathas alla aux champs, selon qu’il était convenu avec David; un petit garçon l’accompagnait.
Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
36 Il dit à son garçon: « Cours, retrouve les flèches que je vais tirer. » Le garçon courut, et Jonathas tira une flèche de manière à le dépasser.
Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
37 Lorsque le garçon arriva à l’endroit de la flèche que Jonathas avait tirée, Jonathas cria après le garçon et dit: « La flèche n’est-elle pas plus loin que toi? »
Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
38 Jonathas cria encore après le garçon: « Vite, hâte-toi, ne t’arrête pas! » Et le garçon de Jonathas ramassa la flèche et revint vers son maître.
Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
39 Le garçon ne savait rien; Jonathas et David seuls comprenaient la chose.
(Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
40 Jonathas donna ses armes au garçon qui était avec lui, et lui dit: « Va, et portes-les à la ville. »
Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
41 Dès que le garçon fut parti, David se leva du côté du midi et, se jetant la face contre terre, il se prosterna trois fois devant Jonathas; puis ils s’embrassèrent l’un l’autre et pleurèrent au sujet l’un de l’autre, au point que David fondit en larmes.
Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
42 Et Jonathas dit à David: « Va en paix, après que nous avons juré l’un et l’autre, au nom de Yahweh, en disant: Que Yahweh soit entre moi et toi, entre ma postérité et ta postérité à jamais! » David se leva et s’en alla, et Jonathas rentra dans la ville.
Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.

< 1 Samuel 20 >