< 1 Samuel 10 >
1 Samuel prit une fiole d’huile, et la versa sur la tête de Saül; puis il le baisa et dit: « Yahweh ne t’a-t-il pas oint pour chef sur son héritage?
Sai Sama’ila ya ɗauki’yar kwalabar mai, ya zuba man ɗin wa Shawulu a kansa, ya yi masa sumba yana cewa, “Ubangiji ya keɓe ka shugaba bisa gādonsa.
2 Quand tu m’auras quitté aujourd’hui, tu trouveras deux hommes près du sépulcre de Rachel, dans le territoire de Benjamin, à Selsach; ils te diront: « Les ânesses que tu es allé chercher sont retrouvées; et voici, ton père a perdu de vue l’affaire des ânesses, mais il est en peine de vous et dit: Que dois-je faire au sujet de mon fils? »
Sa’ad da ka rabu da ni yau, za ka sadu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a Zelza, a yankin Benyamin. Za su ce maka, ‘An sami jakunan da ka fita nema, yanzu haka mahaifinka ya bar damuwa kan jakunan ya koma damuwa a kanka, yana cewa, yaya zan gan ɗana?’
3 De là, poursuivant ta route, tu arriveras au chêne de Thabor, et là tu seras rencontré par trois hommes montant vers Dieu à Béthel, et portant l’un trois chevreaux, l’autre trois miches de pain, et l’autre une outre de vin.
“Sa’an nan za ka ci gaba daga nan sai ka kai wajen babban itace na Tabor. Waɗansu mutum uku za su sadu da kai a hanyarsu zuwa wurin yin wa Allah sujada a Betel. Ɗaya yana ɗauke da’yan awaki uku, ɗaya yana ɗauke da burodi uku, ɗayan kuma yana ɗauke da salkar ruwan inabi.
4 Après qu’ils t’auront salué, ils te donneront deux pains, et tu les recevras de leurs mains.
Za su gaishe ka, su ba ka burodi biyu, kai kuwa sai ka karɓa.
5 Après cela, tu viendras à Gabaa de Dieu, où se trouve un poste de Philistins. En entrant dans la ville, tu rencontreras une troupe de prophètes descendant du haut lieu, précédés de luths, tambourins, flûtes et harpes, et prophétisant.
“Bayan wannan, za ka tafi Gebiya ta Allah, inda sansanin Filistiyawa yake. Kana shiga garin, za ka sadu da jerin gwanon annabawa suna gangarowa daga tudu, ana kaɗa garaya, ana bugan ganguna, ana hura sarewa, ana kuma bugan molo, a gabansu, su kuma za su yi ta annabci.
6 L’Esprit de Yahweh te saisira, et tu prophétiseras avec eux, et tu seras changé en un autre homme.
Ruhun Ubangiji zai sauko a kanka da iko, za ka kuma yi annabci tare da su. Za a canja ka ka zama dabam.
7 Lorsque ces signes se seront accomplis pour toi, fais ce qui se présentera, car Dieu est avec toi.
Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
8 Et tu descendras avant moi à Galgala; et voici, je descendrai vers toi, pour offrir des holocaustes et des sacrifices pacifiques. Tu attendras sept jours jusqu’à ce que je sois venu vers toi et je te ferai connaître ce que tu dois faire. »
“Ka sha gabana zuwa Gilgal. Lalle zan gangara wurinka domin in miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai sai na zo wurinka na kuma gaya maka abin da za ka yi.”
9 Dès que Saül eut tourné le dos pour se séparer de Samuel, Dieu lui donna un autre cœur, et tous ces signes s’accomplirent le même jour.
Da Shawulu ya juya zai bar Sama’ila, sai Allah ya canja wa Shawulu zuciya, alamun nan kuwa suka cika a ranar.
10 Quand ils arrivèrent à Gabaa, voici qu’une troupe de prophètes vint à sa rencontre; et l’Esprit de Dieu le saisit, et il prophétisa au milieu d’eux.
Da suka iso Gibeya, jerin gwanon annabawa suka sadu da shi Ruhun Allah kuma ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga yin annabci tare da su.
11 Quand tous ceux qui le connaissaient auparavant virent qu’il prophétisait avec les prophètes, tous ces gens se dirent l’un à l’autre: « Qu’est-il arrivé au fils de Cis? Saül est-il donc aussi parmi les prophètes? »
Sa’ad da dukan waɗanda suka san shi a dā suka gan shi yana annabci tare da annabawa, sai suka tambayi juna, suka ce, “Me ya faru da ɗan Kish? Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
12 Quelqu’un de la foule prit la parole et dit: « Et qui est leur père? » — C’est pourquoi cela est passé en proverbe: « Saül est-il aussi parmi les prophètes? » —
Wani mutumin da yake zama a can ya ce, “Wane ne kuma mahaifinsu?” Ta haka sai wannan ya zama karin magana cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa?”
13 Lorsqu’il eut cessé de prophétiser, il se rendit en haut lieu.
Bayan da Shawulu ya gama annabci sai ya haura ya tafi tudu.
14 L’oncle de Saül dit à Saül et à son serviteur: « Où êtes-vous allés? » Saül répondit: « Chercher les ânesses; mais ne les ayant vues nulle part, nous sommes allés vers Samuel. »
Sai ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya tambaye shi da baransa ya ce, “Ina kuka je?” Shawulu ya ce, “Mun tafi neman jakuna, amma da ba mu same su ba sai muka tafi wurin Sama’ila.”
15 L’oncle de Saül dit: « Raconte-moi ce que vous a dit Samuel. »
Ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya ce, “Faɗa mini abin da Sama’ila ya ce maka.”
16 Et Saül répondit à son oncle: « Il nous a appris que les ânesses étaient retrouvées. » Mais quant à l’affaire de la royauté, il ne lui rapporta pas ce qu’avait dit Samuel.
Shawulu ya ce, “Ya tabbatar mana cewa an riga an sami jakuna.” Amma bai gaya wa ɗan’uwan mahaifinsa abin da Sama’ila ya ce game da sarauta ba.
17 Samuel convoqua le peuple devant Yahweh à Maspha,
Sama’ila ta tattara mutanen Isra’ila a gaban Ubangiji a Mizfa
18 et il dit aux enfants d’Israël: « Ainsi parle Yahweh, le Dieu d’Israël: J’ai fait monter Israël d’Égypte, et je vous ai délivrés de la main des Égyptiens et de la main de tous les royaumes qui vous opprimaient.
ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na fito da Isra’ila daga Masar, na kuma cece ku daga hannun Masarawa da dukan mulkokin da suka wahalshe ku.’
19 Et vous, aujourd’hui, vous rejetez votre Dieu, qui vous a délivrés de tous vos maux et de toutes vos souffrances, et vous lui dites: Établis un roi sur nous! Présentez-vous maintenant devant Yahweh, selon vos tribus et selon vos familles. »
Amma yanzu kun ƙi Allahnku wanda ya cece ku daga dukan masifu da wahaloli. Kuka ce, ‘Sam, a naɗa mana sarki.’ Saboda haka yanzu sai ku zo gaban Ubangiji kabila-kabila da iyali-iyali.”
20 Samuel fit approcher toutes les tribus d’Israël, et la tribu de Benjamin fut désignée par le sort.
Sa’ad da Sama’ila ya kawo dukan Isra’ila gaba, kabila-kabila, sai aka zaɓi kabilar Benyamin ta wurin jefa ƙuri’a.
21 Il fit approcher la tribu de Benjamin par familles, et la famille de Métri fut désignée; puis Saül, fis de Cis fut désigné. On le chercha, mais on ne le trouva point.
Sai ya kawo kabilar Benyamin gaba, iyali-iyali, aka zaɓi iyalin Matri. A ƙarshe aka zaɓi Shawulu ɗan Kish. Amma da aka neme shi sai ba a same shi ba.
22 Alors ils interrogèrent de nouveau Yahweh: « Est-il venu ici encore quelqu’un? » Yahweh répondit: « Voici, il est caché parmi les bagages. »
Suka ƙara nemi bayani daga Ubangiji suka ce, “Mutumin ya zo nan kuwa?” Ubangiji ya ce, “I, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”
23 On courut le tirer de là, et il se tint au milieu du peuple, dépassant tout le peuple de l’épaule et au delà.
Suka ruga suka kawo shi. Da ya tsaya cikin mutane, sai ya fi kowa tsayi.
24 Et Samuel dit à tout le peuple: « Voyez-vous celui que Yahweh a choisi? Il n’y a personne dans tout le peuple qui soit semblable à lui. » Et tout le peuple poussa des cris en disant: « Vive le roi! »
Sama’ila ya ce wa dukan mutane, “Kun ga wanda Ubangiji ya zaɓa ko? Ba wani kamar sa a cikin dukan mutane.” Sai mutane suka tā da murya suka ce, “Ran sarki yă daɗe.”
25 Alors Samuel exposa au peuple le droit de la royauté, et il l’écrivit dans le livre, qu’il déposa devant Yahweh; puis il renvoya tout le peuple, chacun dans sa maison.
Sama’ila kuwa ya bayyana wa mutane ƙa’idodin sarauta. Ya rubuta su cikin littafi ya ajiye a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya sallame mutane, kowa ya koma gidansa.
26 Saül aussi s’en alla dans sa maison à Gabaa, accompagné d’hommes de valeur, dont Dieu avait touché le cœur.
Shawulu ma ya tafi gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawan da Allah ya taɓa zuciyarsu.
27 Toutefois les hommes de Bélial disaient: « Est-ce celui-là qui nous sauvera? » Et ils le méprisèrent et ne lui apportèrent pas de présents. Mais Saül n’y prit point garde.
Amma waɗansu’yan iska suka ce, “Yaya wannan mutum zai iya cetonmu?” Suka rena shi suka ƙi su kawo masa kyautai. Amma Shawulu bai ce uffam ba.