< 1 Rois 8 >
1 Alors le roi Salomon assembla près de lui à Jérusalem les anciens d’Israël et tous les chefs des tribus, les princes des familles des enfants d’Israël, pour transporter de la cité de David, c’est-à-dire de Sion, l’arche de l’alliance de Yahweh.
Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
2 Tous les hommes d’Israël se réunirent auprès du roi Salomon, au mois d’éthanim, qui est le septième mois, pendant la fête.
Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
3 Lorsque tous les anciens d’Israël furent arrivés, les prêtres portèrent l’arche.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
4 Ils transportèrent l’arche de Yahweh, ainsi que la tente de réunion et tous les ustensiles sacrés qui étaient dans la tente; ce furent les prêtres et les lévites qui les transportèrent.
suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
5 Le roi Salomon et toute l’assemblée d’Israël convoquée auprès de lui se tenaient avec lui devant l’arche. Ils immolèrent des brebis et des bœufs, qui ne pouvaient être ni comptés ni nombrés à cause de leur multitude.
sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
6 Les prêtres portèrent l’arche de l’alliance de Yahweh à sa place, dans le sanctuaire de la maison, dans le Saint des saints, sous les ailes des Chérubins.
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
7 Car les Chérubins étendaient leurs ailes sur la place de l’arche, et les Chérubins couvraient l’arche et ses barres par-dessus.
Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
8 Les barres avaient une longueur telle que leurs extrémités se voyaient du lieu saint devant le sanctuaire, mais on ne les voyait point du dehors. Elles ont été là jusqu’à ce jour.
Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
9 Il n’y avait dans l’arche que les deux tables de pierre, que Moïse y avait déposées sur le mont Horeb, lorsque Yahweh conclut une alliance avec les enfants d’Israël à leur sortie du pays d’Égypte.
Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
10 Au moment où les prêtres sortirent du lieu saint, la nuée remplit la maison de Yahweh.
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11 Les prêtres ne purent pas y rester pour faire leur service, à cause de la nuée; car la gloire de Yahweh remplissait la maison de Yahweh.
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12 Alors Salomon dit: « Yahweh veut habiter dans l’obscurité.
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13 J’ai bâti une maison qui sera votre demeure, un lieu pour que vous y résidiez à jamais. »
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
14 Puis le roi tourna son visage et bénit toute l’assemblée d’Israël, et toute l’assemblée d’Israël était debout.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
15 Et il dit: « Béni soit Yahweh. Dieu d’Israël, qui a parlé par sa bouche à David, mon père, et qui a accompli par sa main ce qu’il avait déclaré en disant:
Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
16 Depuis le jour où j’ai fait sortir d’Égypte mon peuple d’Israël, je n’ai point choisi de ville, parmi toutes les tribus d’Israël, pour qu’on y bâtisse une maison où réside mon nom, mais j’ai choisi David pour qu’il règne sur mon peuple d’Israël.
‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
17 David, mon père, avait l’intention de bâtir une maison au nom de Yahweh, Dieu d’Israël;
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
18 mais Yahweh dit à David, mon père: Puisque tu as eu l’intention de bâtir une maison à mon nom, tu as bien fait d’avoir eu cette intention.
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
19 Seulement, ce ne sera pas toi qui bâtiras la maison; ce sera ton fils, sorti de tes entrailles, qui bâtira la maison à mon nom.
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
20 Yahweh a accompli la parole qu’il avait prononcée: je me suis élevé à la place de David, mon père, et je me suis assis sur le trône d’Israël, comme Yahweh l’avait dit, et j’ai bâti la maison au nom de Yahweh, Dieu d’Israël.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
21 J’y ai établi un lieu pour l’arche où se trouve l’alliance de Yahweh, alliance qu’il a conclue avec nos pères quand il les a fait sortir du pays d’Égypte. »
Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
22 Salomon se plaça devant l’autel de Yahweh, en face de toute l’assemblée d’Israël, et, étendant ses mains vers le ciel,
Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
23 il dit: « Yahweh, Dieu d’Israël, il n’y a point de Dieu semblable à vous, ni en haut dans les cieux, ni en bas sur la terre: à vous, qui gardez l’alliance et la miséricorde envers vos serviteurs qui marchent de tout leur cœur en votre présence;
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
24 comme vous avez gardé à votre serviteur David, mon père, ce que vous lui avez dit; ce que vous avez déclaré par votre bouche, vous l’avez accompli par votre main, comme on le voit en ce jour.
Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
25 Maintenant, Yahweh, Dieu d’Israël, observez en faveur de votre serviteur David, mon père, ce que vous lui avez dit en ces termes: Il ne te manquera jamais devant moi un descendant qui siège sur le trône d’Israël, pourvu que tes fils prennent garde à leur voie, en marchant devant moi comme tu as marché devant moi.
“Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
26 Et maintenant, Dieu d’Israël, qu’elle s’accomplisse donc la parole que vous avez dite à votre serviteur David, mon père!
Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
27 « Mais est-il vrai que Dieu habite sur la terre? Voici que le ciel et le ciel des cieux ne peuvent vous contenir: combien moins cette maison que j’ai bâtie!
“Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
28 Cependant soyez attentif, Yahweh, mon Dieu, à la prière de votre serviteur et à sa supplication, en écoutant le cri joyeux et la prière que votre serviteur prononce devant vous aujourd’hui,
Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
29 en tenant vos yeux ouverts nuit et jour sur cette maison, sur le lieu dont vous avez dit: Là sera mon nom, en écoutant la prière que votre serviteur fait en ce lieu.
Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
30 Écoutez la supplication de votre serviteur et de votre peuple d’Israël, lorsqu’ils prieront en ce lieu; écoutez du lieu de votre demeure, du ciel, écoutez et pardonnez.
Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
31 « Si quelqu’un pèche contre son prochain et qu’on lui fasse prêter un serment, s’il vient jurer devant votre autel, dans cette maison,
“Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
32 écoutez-le du ciel, agissez, et jugez vos serviteurs, condamnant le coupable et faisant retomber sa conduite sur sa tête, déclarant juste l’innocent et lui rendant selon son innocence.
sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
33 « Quand votre peuple d’Israël sera battu devant l’ennemi parce qu’il aura péché contre vous, s’ils reviennent à vous et rendent gloire à votre nom, s’ils vous adressent des prières et des supplications dans cette maison,
“Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
34 écoutez-les du ciel, pardonnez le péché de votre peuple d’Israël, et ramenez-les dans le pays que vous avez donné à leurs pères.
ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
35 « Quand le ciel sera fermé et qu’il n’y aura pas de pluie parce qu’ils auront péché contre vous, s’ils prient dans ce lieu et rendent gloire à votre nom, et s’ils se détournent de leurs péchés, parce que vous les aurez affligés,
“Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
36 écoutez-les du ciel, pardonnez les péchés de vos serviteurs et de votre peuple d’Israël, en leur enseignant la bonne voie dans laquelle ils doivent marcher, et faites tomber la pluie sur la terre que vous avez donnée en héritage à votre peuple.
ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
37 « Quand la famine sera dans le pays, quand il y aura la peste, quand il y aura la rouille, la nielle, la sauterelle, le hasil; quand l’ennemi assiégera votre peuple dans le pays, dans ses portes; quand il y aura fléau ou maladie quelconques,
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
38 si un homme, si tout votre peuple d’Israël fait entendre des prières et des supplications, et que chacun, reconnaissant la plaie de son cœur, étende ses mains vers cette maison,
in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
39 écoutez- les du ciel, du lieu de votre demeure, et pardonnez; agissez et rendez à chacun selon toutes ses voies, vous qui connaissez son cœur, — car seul vous connaissez les cœurs de tous les enfants des hommes, —
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
40 afin qu’ils vous craignent tous les jours qu’ils vivront sur la face du pays que vous avez donné à nos pères.
saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
41 « Quant à l’étranger, qui n’est pas de votre peuple d’Israël, mais qui viendra d’un pays lointain à cause de votre nom,
“Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
42 — car on entendra parler de votre grand nom, de votre main forte et de votre bras étendu, — quand il viendra prier dans cette maison,
gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
43 écoutez- le du ciel, du lieu de votre demeure, et agissez selon tout ce que vous demandera l’étranger, afin que tous les peuples de la terre connaissent votre nom, pour vous craindre, comme votre peuple d’Israël, et qu’ils sachent que votre nom est appelé sur cette maison que j’ai bâtie.
ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
44 « Quand votre peuple sortira pour combattre son ennemi, en suivant la voie dans laquelle vous les aurez envoyés, et qu’ils adresseront des prières à Yahweh, le visage tourné vers la ville que vous avez choisie et vers la maison que j’ai bâtie à votre nom,
“Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
45 écoutez du ciel leur prière et leur supplication, et rendez-leur justice.
ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
46 « Quand ils pécheront contre vous, — car il n’y a pas d’homme qui ne pèche, — et quand, irrité contre eux, vous les livrerez à l’ennemi, et que leur vainqueur les emmènera captifs au pays de l’ennemi, lointain ou rapproché,
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
47 s’ils rentrent en eux-mêmes dans le pays de leurs vainqueurs, s’ils se convertissent et vous adressent des supplications dans le pays de leurs tyrans, en disant: Nous avons péché, nous avons fait l’iniquité, nous avons commis le crime;
in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
48 s’ils reviennent à vous de tout leur cœur et de toute leur âme, dans le pays de leurs ennemis qui les ont emmenés captifs, s’ils vous adressent des prières, le visage tourné vers leur pays que vous avez donné à leurs pères, vers la ville que vous avez choisie et vers la maison que j’ai bâtie à votre nom,
in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
49 écoutez, du ciel, du lieu de votre demeure, leur prière et leur supplication, et faites-leur droit;
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
50 pardonnez à votre peuple ses transgressions et tous ses péchés qu’il a commis contre vous; faites-en un sujet de compassion devant leurs tyrans, afin qu’ ils aient pitié d’eux;
Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
51 car ils sont votre peuple et votre héritage, que vous avez fait sortir d’Égypte, du milieu d’une fournaise de fer:
Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
52 afin que vos yeux soient ouverts à la supplication de votre serviteur et à la supplication de votre peuple d’Israël, pour les écouter en tout ce qu’ils vous demanderont.
“Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
53 Car vous les avez séparés de tous les peuples de la terre pour vous, pour en faire votre héritage, comme vous l’avez déclaré par Moïse, votre serviteur, quand vous avez fait sortir nos pères d’Égypte, ô Seigneur Yahweh. »
Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
54 Lorsque Salomon eut achevé d’adresser à Yahweh toute cette prière et cette supplication, il se leva de devant l’autel de Yahweh, où il était à genoux, les mains étendues vers le ciel.
Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
55 S’étant levé, il bénit toute l’assemblée d’Israël à haute voix en disant:
Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
56 « Béni soit Yahweh qui a donné du repos à son peuple d’Israël, selon tout ce qu’il a dit! De toutes les bonnes paroles qu’il a fait entendre par l’organe de Moïse, son serviteur, aucune parole n’est restée sans effet.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
57 Que Yahweh, notre Dieu, soit avec nous, comme il a été avec nos pères; qu’il ne nous abandonne point et ne nous délaisse point,
Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
58 mais qu’il incline nos cœurs vers lui, afin que nous marchions dans toutes ses voies, et que nous observions ses commandements, ses lois et ses ordonnances, qu’il a prescrits à nos pères.
Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
59 Que mes paroles de supplication que j’ai prononcées devant Yahweh soient proches de Yahweh, notre Dieu, nuit et jour, pour que, selon le besoin de chaque jour, il fasse droit à son serviteur et à son peuple d’Israël,
Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
60 afin que tous les peuples de la terre sachent que Yahweh est Dieu, qu’il n’y en a point d’autre.
saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
61 Que votre cœur soit tout à Yahweh, notre Dieu, pour marcher selon ses lois et pour observer ses commandements, comme nous le faisons aujourd’hui. »
Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
62 Le roi et tout Israël avec lui offrirent des sacrifices devant Yahweh.
Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
63 Salomon immola vingt-deux mille bœufs et cent vingt mille brebis pour le sacrifice pacifique qu’il offrit à Yahweh. C’est ainsi que le roi et tous les enfants d’Israël firent la dédicace de la maison de Yahweh.
Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
64 En ce jour, le roi consacra le milieu du parvis qui est devant la maison de Yahweh; car il offrit là les holocaustes, les oblations et les graisses des sacrifices pacifiques, parce que l’autel d’airain qui est devant Yahweh était trop petit pour contenir les holocaustes, les oblations et les graisses des sacrifices pacifiques.
A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
65 Salomon célébra la fête en ce temps-là, et tout Israël avec lui, grande multitude venue depuis l’entrée d’Emath jusqu’au torrent d’Égypte, — devant Yahweh, notre Dieu, — pendant sept jours et sept autres jours, soit quatorze jours.
Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
66 Le huitième jour il renvoya le peuple. Et ils bénirent le roi, et s’en allèrent dans leurs demeures, joyeux et le cœur content pour tout le bien que Yahweh avait fait à David, son serviteur, et à Israël, son peuple.
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.