< 1 Rois 2 >

1 Comme le temps de sa mort approchait, David donna ses ordres à Salomon, son fils, en disant:
Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
2 « Je m'en vais par le chemin de toute la terre; montre-toi fort et sois un homme!
“Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
3 Garde le service de Yahweh, ton Dieu, en marchant dans ses voies, en observant ses lois, ses commandements, ses ordonnances et ses préceptes, selon ce qui est écrit dans la loi de Moïse, afin que tu réussisses dans tout ce que tu feras et partout où tu te tourneras,
ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
4 en sorte que Yahweh accomplisse sa parole qu'il a prononcée sur moi, en disant: Si tes fils prennent garde à leur voie, en marchant devant moi avec fidélité, de tout leur cœur et de toute leur âme, tu ne manqueras jamais d'un descendant assis sur le trône d'Israël.
Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
5 Tu sais aussi toi-même ce que m'a fait Joab, fils de Sarvia, ce qu'il a fait aux deux chefs des armées d'Israël, à Abner, fils de Ner, et à Amasa, fils de Jéther: il les a tués, versant pendant la paix le sang de la guerre, et mettant le sang de la guerre sur la ceinture qu'il avait aux reins et sur la chaussure qu'il avait aux pieds.
“Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
6 Tu agiras selon ta sagesse, et tu ne laisseras pas ses cheveux blancs descendre en paix au séjour des morts. (Sheol h7585)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
7 Mais aux fils de Berzellaï le Galaadite tu montreras de la bienveillance, et ils seront de ceux qui mangent à ta table; car c'est ainsi qu'ils se sont approchés de moi lorsque je fuyais devant Absalom, ton frère.
“Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
8 Voici que tu as près de toi Séméï, fils de Géra, Benjamite, de Bahurim. Il a proféré contre moi des malédictions violentes le jour où j'allais à Mahanaïm. Mais comme il descendit à ma rencontre vers le Jourdain, je lui jurai par Yahweh, en disant: Je ne te ferai point mourir par l'épée.
“Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
9 Et maintenant, tu ne le laisseras pas impuni; car tu es un homme sage, et tu sais comment tu dois le traiter; c'est dans le sang que tu feras descendre ses cheveux blancs au séjour des morts. » (Sheol h7585)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
10 David se coucha avec ses pères, et il fut enterré dans la cité de David.
Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
11 Le temps que David régna sur Israël fut de quarante ans: il régna sept ans à Hébron, et il régna trente-trois ans à Jérusalem.
Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
12 Et Salomon s'assit sur le trône de David, son père, et son règne fut bien affermi.
Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
13 Adonias, fils de Haggith, vint trouver Bethsabée, mère de Salomon. Elle lui dit: « Viens-tu dans une intention pacifique? » Il répondit: « Oui! dans une intention pacifique; »
To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
14 et il ajouta: « J'ai un mot à te dire. » Elle dit: « Parle. »
Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
15 Et il dit: « Tu sais que le royaume m'appartenait, et que tout Israël portait ses regards sur moi pour que je règne. Mais la royauté a été transférée, et elle a été donnée à mon frère, parce que Yahweh la lui avait destinée.
Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
16 Maintenant, je te demande une seule chose; ne me rejette pas. » Elle lui répondit: « Parle. »
Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
17 Et il dit: « Dis, je te prie, au roi Salomon — car il ne te rejettera pas — de me donner pour femme Abisag, la Sunamite. »
Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
18 Bethsabée dit: « Bien! Je parlerai au roi à ton sujet. »
Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
19 Bethsabée se rendit auprès du roi Salomon pour lui parler au sujet d'Adonias. Et le roi se leva pour aller à sa rencontre et il se prosterna devant elle; il s'assit sur son trône, et fit placer un trône pour la mère du roi, et elle s'assit à sa droite.
Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
20 Puis elle dit: « J'ai une petite demande à te faire: ne me rejette pas. » Le roi lui dit: « Demande, ma mère, car je ne te rejetterai pas. »
Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
21 Elle dit: « Qu'Abisag, la Sunamite, soit donnée pour femme à Adonias, ton frère. »
Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
22 Le roi Salomon répondit et dit à sa mère: « Pourquoi demandes-tu Abisag, la Sunamite, pour Adonias? Demande donc la royauté pour lui, — car il est mon frère aîné, — pour lui, pour le prêtre Abiathar, et pour Joab, fils de Sarvia! »
Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
23 Le roi Salomon jura par Yahweh, en disant: « Que Dieu me traite dans toute sa rigueur si ce n'est pas pour sa perte qu'Adonias a prononcé cette parole!
Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
24 Et maintenant, Yahweh est vivant! — lui qui m'a affermi et m'a fait asseoir sur le trône de David, mon père, et qui m'a édifié une maison selon qu'il l'avait dit, — aujourd'hui même, Adonias sera mis à mort! »
Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
25 Et le roi Salomon députa Banaïas, fils de Joïadas; il frappa Adonias, qui mourut.
Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
26 Le roi dit au prêtre Abiathar: « Va-t'en à Anathoth dans tes terres, car tu mérites la mort; mais je ne te ferai pas mourir aujourd'hui, parce que tu as porté l'arche du Seigneur Yahweh devant David, mon père, et parce que tu as eu ta part dans tout ce qu'a souffert mon père. »
Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
27 Et Salomon chassa Abiathar pour qu'il ne fût plus prêtre de Yahweh, accomplissant ainsi la parole que Yahweh avait prononcée sur la maison d'Héli à Silo.
Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
28 La nouvelle en parvint à Joab, car Joab avait suivi le parti d'Adonias, quoiqu'il n'eût pas suivi le parti d'Absalom. Et Joab s'enfuit au tabernacle de Yahweh, et il saisit les cornes de l'autel.
Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
29 On annonça au roi Salomon que Joab s'était réfugié au tabernacle de Yahweh et qu'il était auprès de l'autel; et Salomon envoya Banaïas, fils de Joïadas, en lui disant: « Va, frappe-le. »
Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
30 Arrivé au tabernacle de Yahweh, Banaïas dit à Joab: « Ainsi parle le roi: Sors. » Mais il répondit: « Non! je mourrai ici. » Banaïas rapporta cette réponse au roi, en disant: « C'est ainsi qu'a parlé Joab, c'est ainsi qu'il m'a répondu. »
Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
31 Et le roi dit à Banaïas: « Fais comme il a dit, frappe-le et enterre-le; tu ôteras ainsi de dessus moi et de dessus la maison de mon père le sang que Joab a répandu sans raison.
Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
32 Yahweh fera retomber son sang sur sa tête, lui qui a frappé deux hommes plus justes et meilleurs que lui, et qui les a tués par l'épée, sans que mon père David le sût: Abner, fils de Ner, chef de l'armée d'Israël, et Amasa, fils de Jéther, chef de l'armée de Juda.
Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
33 Leur sang retombera sur la tête de Joab et sur la tête de ses descendants à jamais; mais il y aura paix pour toujours, de la part de Yahweh, pour David et sa postérité, pour sa maison et son trône. »
Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
34 Banaïas, fils de Joïadas, monta et, ayant frappé Joab, il lui donna la mort, et il fut enterré dans sa maison, au désert.
Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
35 Et le roi mit à sa place, comme chef de l'armée, Banaïas, fils de Joïadas; et le roi mit le prêtre Sadoc à la place d'Abiathar.
Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
36 Le roi envoya appeler Séméï et lui dit: « Bâtis-toi une maison à Jérusalem; tu y demeureras et tu n'en sortiras point pour aller de côté et d'autre.
Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
37 Le jour où tu sortiras et passeras le torrent de Cédron, sache bien que certainement tu mourras; ton sang sera sur ta tête. »
Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
38 Séméï répondit au roi: « Cette parole est bonne; ce que dit mon seigneur le roi, ton serviteur le fera. » Et Séméï demeura de nombreux jours à Jérusalem.
Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
39 Il arriva, au bout de trois ans, que deux serviteurs de Séméï s'enfuirent auprès d'Achis, fils de Maacha, roi de Geth. On le rapporta à Séméï, en disant: « Voici que tes serviteurs sont à Geth. »
Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
40 Séméï se leva et, ayant sellé son âne, il se rendit à Geth, auprès d'Achis, pour chercher ses serviteurs. Séméï s'en alla et ramena de Geth ses serviteurs.
Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
41 On rapporta à Salomon que Séméï était allé de Jérusalem à Geth et qu'il était de retour.
Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
42 Le roi envoya appeler Séméï et lui dit: « Ne t'avais-je pas fait jurer par Yahweh, et ne t'avais-je pas fait une injonction en disant: Le jour où tu sortiras pour aller de côté ou d'autre, sache bien que certainement tu mourras? Et ne m'as-tu pas répondu: La parole que j'ai entendue est bonne?
Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
43 Pourquoi donc n'as-tu pas observé le serment fait à Yahweh et l'ordre que je t'avais donné? »
To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
44 Et le roi dit à Séméï: « Tu sais — ton cœur le sait — tout le mal que tu as fait à David, mon père; Yahweh fait retomber ta méchanceté sur ta tête.
Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
45 Mais le roi Salomon sera béni, et le trône de David sera affermi à jamais devant Yahweh. »
Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
46 Et le roi donna des ordres à Banaïas, fils de Joïadas; et il sortit et frappa Séméï, qui mourut. Et la royauté fut affermie entre les mains de Salomon.
Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.

< 1 Rois 2 >