< 1 Chroniques 29 >

1 Le roi David dit à toute l’assemblée: « Mon fils Salomon, le seul que Dieu ait choisi, est jeune et faible, et l’ouvrage est considérable; car ce palais n’est pas pour un homme, mais pour Yahweh Dieu.
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
2 J’ai mis tous mes efforts à préparer pour la maison de mon Dieu de l’or pour les objets d’or, de l’argent pour les objets d’argent, de l’airain pour les objets d’airain, du fer pour les objets de fer, du bois pour les objets de bois, des pierres d’onyx et des pierres à enchâsser, des pierres d’ornement et de diverses couleurs, toutes sortes de pierres précieuses et des pierres de marbre en abondance.
Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
3 De plus, dans mon affection pour la maison de Dieu, l’or et l’argent que je possède en propre, je le donne à la maison de mon Dieu, outre tout ce que j’ai préparé pour la maison du sanctuaire:
Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
4 trois mille talents d’or, d’or d’Ophir, et sept mille talents d’argent épuré, pour en revêtir les parois des chambres,
talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
5 l’or pour les objets d’or, l’argent pour les objets d’argent, et pour tous les travaux de la main des ouvriers. Qui veut aujourd’hui remplir spontanément sa main d’offrandes pour Yahweh? »
don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
6 Les chefs des familles, les princes des tribus d’Israël, les chefs de milliers et de centaines, ainsi que les intendants du roi, firent volontairement des offrandes.
Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
7 Ils donnèrent pour le travail de la maison de Dieu cinq mille talents d’or, dix mille dariques, dix mille talents d’argent, dix-huit mille talents d’airain et cent mille talents de fer.
Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
8 Ceux qui possédaient des pierres précieuses les donnèrent, pour le trésor de la maison de Yahweh, entre les mains de Jahiel, le Gersonite.
Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
9 Le peuple se réjouit de leurs offrandes volontaires, car c’était d’un cœur parfait qu’ils faisaient ces offrandes volontaires à Yahweh; le roi David en eut aussi une grande joie.
Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
10 David bénit Yahweh aux yeux de toute l’assemblée; et David dit: « Béni soyez-vous, d’éternité en éternité, Yahweh, Dieu de notre père d’Israël!
Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
11 À vous, Yahweh, la grandeur, la puissance, la magnificence, la splendeur et la gloire, car tout, au ciel et sur la terre, vous appartient; à vous, Yahweh, la royauté; à vous de vous élever souverainement au-dessus de tout.
Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
12 De vous dérivent la richesse et la gloire; vous dominez sur tout; dans votre main est la force et la puissance, et à votre main il appartient de donner à toutes choses grandeur et solidité.
Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
13 Maintenant donc, ô notre Dieu, nous vous louons et nous célébrons votre nom glorieux.
Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
14 Car qui suis-je et qui est mon peuple, que nous ayons le pouvoir et la force de faire volontairement de pareilles offrandes? Tout vient de vous, et nous vous donnons ce que nous avons reçu de votre main.
“Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
15 Car nous sommes devant vous des étrangers et des colons, comme l’étaient tous nos pères; nos jours sur la terre sont comme l’ombre, et il n’y a pas d’espoir.
Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
16 Yahweh, notre Dieu, toutes ces richesses que nous avons préparées pour vous bâtir une maison pour votre saint nom, c’est de votre main qu’ elles viennent, et c’est à vous que tout appartient.
Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
17 Je sais, ô mon Dieu, que vous sondez les cœurs et que vous aimez la droiture; aussi j’ai fait volontairement toutes ces offrandes dans la droiture de mon cœur, et je vois maintenant avec joie votre peuple qui se trouve ici vous faire volontairement ses offrandes.
Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
18 Yahweh, Dieu d’Abraham, d’Isaac et d’Israël, nos pères, gardez à jamais cette disposition comme la forme des sentiments du cœur de votre peuple, et tenez leur cœur tourné vers vous.
Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
19 Et à mon fils Salomon donnez un cœur parfait pour observer vos commandements, vos préceptes et vos lois, pour les mettre tous en pratique et pour bâtir le palais pour lequel j’ai fait des préparatifs. »
Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
20 David dit à toute l’assemblée: « Bénissez donc Yahweh, votre Dieu. » Et toute l’assemblée bénit Yahweh, le Dieu de leurs pères; ils s’inclinèrent et se prosternèrent devant Yahweh et devant le roi.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
21 Le lendemain de ce jour, ils immolèrent des victimes à Yahweh, et offrirent en holocauste à Yahweh mille taureaux, mille béliers et mille agneaux, avec les libations ordinaires, et d’ autres sacrifices en grand nombre pour tout Israël;
Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
22 ils mangèrent et burent ce jour-là devant Yahweh avec une grande joie. Pour la seconde fois, ils proclamèrent roi Salomon, fils de David, et l’oignirent comme chef devant Yahweh; et ils oignirent Sadoc comme grand prêtre.
Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
23 Salomon s’assit sur le trône de Yahweh comme roi, à la place de David, son père; il prospéra, et tout Israël lui obéit.
Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
24 Tous les chefs et les vaillants, même tous les fils du roi David, se soumirent au roi Salomon.
Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
25 Yahweh éleva au plus haut degré la grandeur de Salomon sous les yeux de tout Israël, et il donna à son règne une gloire que n’eut jamais avant lui aucun roi en Israël.
Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
26 David, fils d’Isaï, régna sur tout Israël.
Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
27 Le temps qu’il régna sur Israël fut de quarante ans; il régna sept ans à Hébron, et il régna trente-trois ans à Jérusalem.
Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
28 Il mourut dans une heureuse vieillesse, rassasié de jours, de richesse et de gloire; et Salomon, son fils, régna à sa place.
Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Les actions du roi David, les premières et les dernières, voici qu’elles sont écrites dans l’histoire de Samuel le voyant, dans l’histoire de Nathan le prophète et dans l’histoire de Gad le voyant,
Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
30 avec tout son règne et tous ses exploits et les vicissitudes qui lui sont survenues, ainsi qu’à Israël, et à tous les royaumes des autres pays.
tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.

< 1 Chroniques 29 >