< 1 Chroniques 19 >
1 Après cela, Naas, roi des fils d’Ammon, mourut, et son fils régna à sa place.
Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 David dit: « Je montrerai de la bienveillance à Hanon, fils de Naas, car son père m’a montré de la bienveillance. » Et David envoya des messagers pour le consoler au sujet de son père. Lorsque les serviteurs de David furent arrivés, dans le pays des fils d’Ammon, auprès de Hanon, pour le consoler,
Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
3 les princes des fils d’Ammon dirent à Hanon: « Penses-tu que ce soit pour honorer ton père que David t’envoie des consolateurs? N’est-ce pas pour reconnaître et détruire, et pour explorer le pays, que ses serviteurs sont venus vers toi! »
sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
4 Alors Hanon, ayant saisi les serviteurs de David, les rasa et coupa leurs habits à mi-hauteur, jusqu’à la hanche, et il les renvoya.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
5 On alla informer David de ce qui était arrivé à ses hommes, et il envoya des gens à leur rencontre, car ces hommes étaient dans une grande confusion, et le roi leur fit dire: « Restez à Jéricho, jusqu’à ce que votre barbe ait repoussé, et vous reviendrez ensuite. »
Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
6 Les fils d’Ammon virent qu’ils s’étaient rendus odieux à David, et Hanon et les fils d’Ammon envoyèrent mille talents d’argent pour prendre à leur solde des chars et des cavaliers chez les Syriens de Mésopotamie et chez les Syriens de Maacha et de Soba.
Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
7 Ils prirent à leur solde trente-deux mille chars, et le roi de Maacha avec son peuple, lesquels vinrent camper près de Médaba. Les fils d’Ammon se rassemblèrent de leurs villes et vinrent au combat.
Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
8 David l’apprit et fit partir contre eux Joab et toute l’armée, les hommes vaillants.
Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
9 Les fils d’Ammon sortirent et se rangèrent en bataille à la porte de la ville; les rois qui étaient venus étaient à part dans la campagne.
Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
10 Lorsque Joab vit qu’il y avait un front de bataille devant et derrière lui, il choisit parmi toute l’élite d’Israël un corps qu’il rangea en face des Syriens,
Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
11 et il mit le reste du peuple sous le commandement de son frère Abisaï, les rangeant en face des fils d’Ammon. Il dit:
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
12 « Si les Syriens sont plus forts que moi, tu viendras à mon secours; et si les fils d’Ammon sont plus forts que toi, je te secourrai.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
13 Sois ferme, et combattons vaillamment pour notre peuple et pour les villes de notre Dieu, et que Yahweh fasse ce qui semblera bon à ses yeux! »
Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
14 Joab s’avança donc, ainsi que le peuple qui était avec lui, contre les Syriens pour les attaquer, et ceux-ci s’enfuirent devant lui.
Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
15 Les fils d’Ammon, voyant que les Syriens avaient pris la fuite, s’enfuirent, eux aussi, devant Abisaï, frère de Joab, et rentrèrent dans la ville. Et Joab rentra dans Jérusalem.
Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
16 Les Syriens, voyant qu’ils avaient été battus devant Israël, envoyèrent des messagers pour faire venir les Syriens qui étaient de l’autre côté du fleuve; et Sophach, chef de l’armée d’Hadarézer marchait devant eux.
Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
17 David en reçut la nouvelle et, ayant assemblé tout Israël, il passa le Jourdain, vint vers eux, et disposa l’attaque contre eux; et David rangea son armée en bataille contre les Syriens. Ceux-ci engagèrent le combat contre lui,
Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
18 mais les Syriens s’enfuirent devant Israël, et David tua aux Syriens les chevaux de sept mille chars et quarante mille hommes de pied; il mit aussi à mort Sophach, chef de l’armée.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
19 Les vassaux d’Hadarézer, se voyant battus devant Israël, firent la paix avec David et lui furent assujettis. Et les Syriens ne voulurent plus porter secours aux fils d’Ammon.
Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.