< 1 Chroniques 10 >

1 Les Philistins ayant livré bataille à Israël, les hommes d’Israël prirent la fuite devant les Philistins, et tombèrent blessés à mort sur la montagne de Gelboé.
To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
2 Les Philistins s’attachèrent à poursuivre Saül et ses fils, et les Philistins tuèrent Jonathas, Abinadab et Melchisua, fils de Saül.
Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
3 L’effort du combat se porta sur Saül; les archers l’ayant découvert, il eut grandement peur des archers.
Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
4 Alors Saül dit à son écuyer: « Tire ton épée et m’en transperce, de peur que ces incirconcis ne viennent m’outrager. « L’écuyer ne le voulut pas faire, car il était saisi de crainte; alors Saül prit son épée et se jeta dessus.
Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
5 L’écuyer, voyant que Saül était mort, se jeta aussi sur son épée, et mourut.
Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
6 Ainsi périrent Saül et ses trois fils, et toute sa maison périt en même temps.
Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
7 Tous les hommes d’Israël qui étaient dans la plaine, voyant que les enfants d’Israël s’étaient enfuis, et que Saül et ses fils étaient morts, abandonnèrent leurs villes et prirent aussi la fuite; et les Philistins vinrent et s’y établirent.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
8 Le lendemain, les Philistins vinrent pour dépouiller les morts, et ils trouvèrent Saül et ses fils gisant sur la montagne de Gelboé.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
9 L’ayant dépouillé, ils emportèrent sa tête et ses armes; puis ils envoyèrent publier cette bonne nouvelle par tout le pays des Philistins, devant leurs idoles et le peuple.
Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
10 Ils mirent les armes de Saül dans la maison de leur dieu, et ils attachèrent son crâne dans le temple de Dagon.
Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
11 Tout Jabès en Galaad ayant appris tout ce que les Philistins avaient fait à Saül,
Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
12 tous les vaillants hommes se levèrent, prirent le corps de Saül et les corps de ses fils, et les transportèrent à Jabès. Ils enterrèrent leurs os sous le térébinthe, à Jabès, et ils jeûnèrent sept jours.
sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
13 Saül mourut à cause de la transgression dont il s’était rendu coupable envers Yahweh, parce qu’il n’avait pas observé la parole de Yahweh, et pour avoir interrogé et consulté ceux qui évoquent les morts.
Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
14 Il ne consulta point Yahweh, et Yahweh le fit mourir, et il transféra la royauté à David, fils d’Isaï.
bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.

< 1 Chroniques 10 >