< Zacharie 8 >

1 La parole de Yahweh des armées se fit entendre en ces termes:
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
2 Ainsi parle Yahweh des armées: Je suis animé pour Sion d’un grand zèle; je suis animé pour elle d’une grande fureur.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
3 Ainsi parle Yahweh: Je suis revenu à Sion et je veux habiter au milieu de Jérusalem; Jérusalem sera appelée la ville de vérité, et la montagne de Yahweh des armées, montagne de sainteté.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
4 Ainsi parle Yahweh des armées: Il y aura de nouveau des vieillards et des femmes âgées assis sur les places de Jérusalem, chacun son bâton à la main, à cause du grand nombre de leurs jours.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
5 Les places de la ville seront remplies de jeunes garçons et de jeunes filles jouant sur ses places.
Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
6 Ainsi parle Yahweh des armées: Si cela paraît merveilleux aux yeux du reste de ce peuple, en ces jours-là, cela sera-t-il merveilleux aussi à mes yeux, — oracle de Yahweh des armées?
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
7 Ainsi parle Yahweh des armées: Voici que je vais délivrer mon peuple du pays de l’orient et du pays du soleil couchant.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
8 Je les amènerai et ils habiteront au milieu de Jérusalem; ils seront mon peuple, et moi je serai leur Dieu, avec vérité et justice.
Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
9 Ainsi parle Yahweh des armées: Que vos mains se fortifient, vous qui entendez en ces jours ces paroles de la bouche des prophètes qui ont parlé au jour où fut fondée la maison de Yahweh des armées, pour que le temple soit rebâti.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
10 Car, avant ces jours-là, il n’y avait pas de salaire pour les hommes, pas de salaire pour le bétail, pas de sûreté contre l’ennemi pour ceux qui sortaient et entraient, et j’avais lâché tous les hommes les uns contre les autres.
Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
11 Mais maintenant, je ne suis plus, moi, à l’égard du reste de ce peuple comme aux jours d’autrefois, — oracle de Yahweh des armées.
Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 Car la semence prospérera, la vigne donnera son fruit, la terre donnera ses produits, les cieux donneront leur rosée, et je mettrai le reste de ce peuple en possession de toutes ces choses.
“Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
13 Et il arrivera: comme vous avez été malédiction parmi les nations, maison de Juda et maison d’Israël, ainsi je vous délivrerai, et vous serez bénédiction! Ne craignez point, que vos mains se fortifient!
Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
14 Car ainsi parle Yahweh des armées: Comme J’ai eu le dessein de vous faire du mal lorsque vos pères provoquaient ma colère, dit Yahweh des armées, et que je ne m’en suis pas repenti,
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
15 ainsi j’ai en ces jours-ci, au contraire, le dessein de faire du bien à Jérusalem et à la maison de Juda; ne craignez point!
kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
16 Voici les paroles que vous observerez: Dites la vérité, chacun à votre prochain; rendez la justice dans vos portes selon la vérité et pour la paix;
Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
17 ne méditez pas dans vos cœurs le mal les uns des autres; et n’aimez pas le faux serment; car ce sont là toutes choses que je hais, — oracle de Yahweh.
kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
18 La parole de Yahweh des armées me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
19 Ainsi parle Yahweh des armées: Le jeûne du quatrième mois, le jeûne du cinquième, le jeûne du septième et le jeûne du dixième mois seront changés pour la maison de Juda en réjouissance et en allégresse, et en solennités joyeuses.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
20 Ainsi parle Yahweh des armées: Il viendra encore des peuples et des habitants d’un grand nombre de villes.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
21 Les habitants de l’une iront à l’autre, en disant: « Allons, allons implorer Yahweh et chercher Yahweh des armées! » — « Moi aussi, je veux aller! »
mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
22 Des peuples nombreux et de puissantes nations viendront chercher Yahweh des armées à Jérusalem et implorer Yahweh.
Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
23 Ainsi parle Yahweh des armées: En ces jours-là, dix hommes de toutes les langues des nations saisiront, oui, saisiront le pan de la robe d’un Juif en disant: Nous voulons aller aussi avec vous, car nous avons appris que Dieu est avec vous. »
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”

< Zacharie 8 >