< Zacharie 4 >

1 L’ange qui parlait avec moi revint, et il me réveilla comme un homme qui se réveille de son sommeil.
Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
2 Et il me dit: « Que vois-tu? » Je répondis: « J’ai vu, et voici un candélabre tout en or, avec son bassin à son sommet, portant ses sept lampes avec sept conduits pour les lampes qui sont au sommet du candélabre.
Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
3 Et deux oliviers sont à côté de lui, l’un à droite du bassin, et l’autre à sa gauche. »
Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
4 Et je repris la parole et je dis à l’ange qui parlait avec moi: « Que sont ces choses, mon seigneur? »
Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
5 L’ange qui parlait avec moi me répondit et me dit: « Ne sais-tu pas ce que sont ces choses? » Je répondis: « Non, mon seigneur. »
Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
6 Et il reprit et me dit: Ceci est la parole de Yahweh à Zorobabel, savoir: « Ni par une armée, ni par la force, mais par mon Esprit, dit Yahweh des armées.
Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
7 Qui es-tu, grande montagne, devant Zorobabel? Tu seras une plaine. Et il élèvera la pierre du sommet au milieu des acclamations: Grâce, grâce sur elle! »
“Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
8 La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
9 « Les mains de Zorobabel ont fondé cette maison, et ses mains l’achèveront, et tu sauras que Yahweh des armées m’a envoyé vers vous.
“Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
10 Car qui mépriserait le temps des petites choses? Ils se réjouiront en voyant le fil à plomb dans la main de Zorobabel. » « Ces sept lampes sont les yeux de Yahweh, qui parcourent toute la terre »
“Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
11 Je repris la parole et je lui dis: « Que sont ces deux oliviers à la droite du candélabre et à sa gauche? »
Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
12 Je repris une seconde fois la parole et lui dis: « Que sont ces deux grappes d’olivier qui se trouvent auprès des deux entonnoirs d’or d’où l’or découle? »
Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
13 Il me parla en ces termes: « Ne sais-tu pas ce que c’est? » Je répondis: « Non, mon seigneur. »
Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
14 Et il me dit: « Ce sont les deux fils de l’onctionqui se tiennent près du Seigneur de toute la terre. »
Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”

< Zacharie 4 >