< Zacharie 10 >

1 Demandez à Yahweh de la pluie au printemps. C’est Yahweh qui fait les éclairs; il leur donnera une pluie abondante, à chacun de l’herbe dans son champ.
Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
2 Car les théraphim ont parlé futilité, et les devins ont eu des visions de mensonge; ils débitent de vains songes, et donnent de fausses consolations. C’est pourquoi ils sont partis comme un troupeau; ils ont été opprimés, faute de berger.
Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
3 Ma colère s’est enflammée contre les bergers, et je châtierai les boucs! Car Yahweh des armées visite son troupeau, la maison de Juda, et il en fait son cheval d’honneur dans la bataille.
“Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
4 De lui viendra la troupe, de lui le pieu, de lui l’arc de guerre; de lui sortiront tous les chefs ensemble.
Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
5 Ils seront comme des héros, foulant la boue des chemins dans la bataille; ils combattront, car Yahweh sera avec eux, et ils couvriront de honte ceux qui sont montés sur des chevaux.
Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
6 Je fortifierai la maison de Juda, et je sauverai la maison de Joseph; je les rétablirai, car j’ai compassion d’eux, et ils seront comme si je ne les avais pas rejetés. Car moi, je suis Yahweh, leur Dieu, et je les exaucerai.
“Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
7 Ceux d’Ephraïm seront comme des héros, et leur cœur sera joyeux comme par le vin; leurs fils le verront et se réjouiront, et leur cœur tressaillira en Yahweh.
Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
8 Je sifflerai après eux, et je les rassemblerai, car je les ai rachetés, et ils se multiplieront comme ils s’étaient multipliés.
Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
9 Quand je les aurai répandus parmi les peuples, et qu’ils se souviendront de moi dans les pays lointains, ils vivront avec leurs enfants et ils reviendront.
Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
10 Je les ramènerai du pays d’Égypte, et je les rassemblerai d’Assyrie, et je les ferai venir au pays de Galaad et au Liban, et il ne se trouvera pas assez d’espace pour eux.
Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
11 Il passera par la mer, mer de détresse, il frappera les flots dans la mer, et toutes les profondeurs du fleuve seront mises à sec. L’orgueil de l’Assyrie sera abattu, et le sceptre de l’Égypte sera ôté.
Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
12 Je les fortifierai en Yahweh, et ils marcheront en son nom, — oracle de Yahweh.
Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.

< Zacharie 10 >